< Hioba 32 >

1 A [gdy] ci trzej mężczyźni przestali odpowiadać Hiobowi, ponieważ był sprawiedliwy we własnych oczach;
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Wtedy zapłonął gniewem Elihu, syn Barakeela, Buzyta, z rodu Ram; rozgniewał się na Hioba, gdyż usprawiedliwiał siebie bardziej niż Boga.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 Rozpalił się także jego gniew na jego trzech przyjaciół, bo nie znaleźli żadnej odpowiedzi, a jednak potępiali Hioba.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Elihu czekał, aż Hiob skończy odpowiedź, gdyż oni byli od niego starsi.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 Gdy Elihu zauważył, że w ustach trzech mężczyzn nie ma żadnej odpowiedzi, zapłonął gniewem.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 I Elihu, syn Barakeela, Buzyta, odpowiedział: Ja jestem młody, a wy jesteście starzy, dlatego bałem się i nie śmiałem wyjawić wam swego zdania.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 Myślałem: Niech przemówią dni, a mnogość lat [niech] uczy mądrości.
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Ale to duch jest w człowieku i tchnienie Wszechmogącego daje rozum.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 Wielcy nie [zawsze są] mądrzy, a starcy nie [zawsze] rozumieją sąd.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Dlatego mówię: Posłuchajcie mnie, ja też wypowiem swoje zdanie.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Oto czekałem na wasze słowa, przysłuchiwałem się waszym dowodom, gdy przygotowywaliście mowę.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 I przypatrywałem się wam, a oto żaden z was nie przekonał Hioba i nikt nie odpowiedział na jego słowa;
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 I nie możecie powiedzieć: Znaleźliśmy mądrość. [Sam] Bóg go strąca, nie człowiek.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Nie do mnie skierował swoje słowa, a ja nie odpowiem mu waszymi słowami.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 Zaniepokoili się i już nie odpowiadali; przestali mówić.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 Czekałem, lecz nie mówili, ale stanęli i już nic nie powiedzieli.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 Odpowiem ze swojej strony, wypowiem też swoje zdanie.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Jestem bowiem pełny słów, mój duch przymusza mnie.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Oto moje wnętrze jest jak wino, które nie ma ujścia; jak nowe bukłaki [zagrożone] pęknięciem.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 Będę więc mówić, aby ulżyć sobie; otworzę swoje wargi i odpowiem.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Nie będę miał względu na nikogo i nikomu nie będę schlebiał.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 Nie umiem bowiem schlebiać, gdyż mój Stwórca wnet by mnie porwał.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< Hioba 32 >