< Izajasza 55 >

1 Nuż wszyscy pragnący pójdźcie do wód, i wy, co niemacie pieniędzy, pójdźcie, kupujcie a jedzcie; pójdźcie, mówię, kupujcie bez pieniędzy i bez zapłaty, wino i mleko.
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
2 Przecz wynakładacie pieniądze nie za chleb, a pracę swą na to, co nie nasyca? Słuchając słuchajcie mię, a jedzcie to, co jest dobrego, i niech się rozkocha w tłustości dusza wasza.
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
3 Nakłońcie ucha swego, a pójdźcie do mnie; słuchajcie, a będzie żyła dusza wasza. I postanowię z wami przymierze wieczne, miłosierdzie Dawidowe pewne wyleję na was.
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
4 Oto dałem go za świadka narodom, za wodza i za nauczyciela narodom.
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
5 Oto naród, któregoś nie znał, powołasz, a narody, które cię nie znały, zbieżą się do ciebie dla Pana, Boga twego, i Świętego Izraelskiego; bo cię uwielbi.
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
6 Szukajcie Pana, póki może być znaleziony; wzywajcie go, póki blisko jest.
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
7 Niech opuści niepobożny drogę swoję, a człowiek nieprawy myśli swoje i niech się nawróci do Pana, a zmiłuje się; i do Boga naszego, gdyż jest hojnym w odpuszczaniu.
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
8 Boć zaiste myśli moje nie są jako myśli wasze, ani drogi wasze jako drogi moje, mówi Pan;
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
9 Ale jako wyższe są niebiosa niż ziemia, tak przewyższają drogi moje drogi wasze, a myśli moje myśli wasze.
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
10 Bo jako zstępuje deszcz i śnieg z nieba, a tam się więcej nie wraca, ale napawa ziemię, a czyni ją płodną, czyni ją też urodzajną, tak że wydaje nasienie siejącemu, a chleb jedzącemu:
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
11 Takci będzie słowo moje, które wynijdzie z ust moich; nie wróci się do mnie próżno, ale uczyni to, co mi się podoba, i poszczęści mu się w tem, na co je poślę.
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
12 Przetoż w weselu wynijdziecie, a w pokoju doprowadzeni będziecie. Góry i pagórki chwałę przed wami głośno zaśpiewają, a wszystkie drzewa polne rękami klaskać będą.
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
13 Miasto ciernia wyrośnie jedlina, a miasto pokrzywy wyrośnie mirt; a to będzie Panu ku sławie, na znak wieczny, który nigdy nie będzie wygładzony.
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< Izajasza 55 >