< Kaudial 3 >

1 INTIN won tounlan en momodijou en Jardej: let majan en me Nen en Kot iju o uju iju mi re a: I aja om wiawia kan, o me mar en maur mi re om, a jo, koe melar.
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Sardis, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi, na wanda yake riƙe da ruhohi bakwai na Allah da kuma taurari bakwai. Na san ayyukanka; ana ganinka kamar rayayye, amma kai matacce ne.
2 Pirida, katene me lua, me nok mela, pwe I jota diaradar, me om wiawia kan unjokela ren ai Kot.
Ka farka! Ka ƙarfafa abin da ya rage wanda kuma yake bakin mutuwa, don ban ga ayyukanka cikakke ne ba a gaban Allahna.
3 I me koe en tamanda, duen koe tunoler, o roner, o kanekid, o kalula. Ma koe jota pan pirida, I pan pwarado due lipirap amen, o koe pan jaja auer, me I pan pwara don uk.
Saboda haka, ka tuna fa, abin da ka karɓa ka kuma ji; ka yi biyayya da shi, ka kuma tuba. Amma in ba ka farka ba, zan zo kamar ɓarawo, ba kuwa za ka san lokacin da zan zo maka ba.
4 A mar malaulau mi re om nan Jardej, me jota kapwelepwel lar ar likau kan, re pan alialu re i nan likau puetepuet, pwe re kon on.
Duk da haka kana da mutane kima cikin Sardis waɗanda ba su ɓata tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni, saye da fararen tufafi, don sun cancanta.
5 Me dadaurata, pan kapwad kida likau puetepuet, o I jota pan irije jan nan puk en maur mar a. O I pan kadede mar a mon Jam ni o mon na tounlan kan.
Wanda ya ci nasara, kamar su, za a sanya masa fararen tufafi. Ba zan taɓa share sunansa daga cikin littafin rai ba, sai dai zan shaida sunansa a gaban Ubana da mala’ikunsa.
6 Me jalon a mia en ron, me Nen o majani on momodijou kan!
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
7 Intin won tounlan en momodijou en Piladelpia: let majan en me jaraui, me melel, me men kapir en Dawid mi re a, me kin ritinida, o jota amen, me kak ritinidi, o me kin ritinidi, o jota amen, me kak ritinida.
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Filadelfiya, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi, na wanda yake mai tsarki da kuma gaskiya, wanda yake riƙe da mabuɗin Dawuda. Abin da ya buɗe ba mai rufewa, abin da kuma ya rufe ba mai buɗewa.
8 I aja om wiawia kan. Kilan, I ki on uk er wanim ritidar eu o jota amen, me kak ritinidi, pwe om kel me tikitik, o koe kin Kanekid ai majan, o koe jota kamam kidar mar ai.
Na san ayyukanka. Duba, na sa a gabanka buɗaɗɗen ƙofa wadda ba mai iya rufewa. Na san cewa kana da ɗan ƙarfi, duk da haka ka kiyaye maganata ba ka kuwa yi mūsun sunana ba.
9 Kilan, I kanain kin uk akai, me udan pwin en Jatan, kijan irail, me akajuj, a jo, re likam. Kilan, I pan kainon ir do, en poni ni na om, o ren aja, me I kin pok on uk.
Zan sa waɗanda suke na majami’ar Shaiɗan, waɗanda suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, sai dai maƙaryata, zan sa su zo su fāɗi a ƙasa a gabanka su kuma shaida cewa na ƙaunace ka.
10 Aki om kanekid ai majan en kanonama, I pil pan kanekid uk ni auer en kajonejon, me pan udon toun jappa karoj, en kajonejon irail, me kaujon jappa.
Da yake ka kiyaye umarnina ta wurin jimrewa, ni ma zan tsare ka daga lokacin nan na gwaji wanda zai zo bisan dukan duniya don a gwada waɗanda suke zama a duniya.
11 I pan pwarado madan. Kolekol, me koe anekier, pwe jota amen en kulia jan mar om.
Ina zuwa ba da daɗewa ba. Ka riƙe abin da kake da shi, don kada wani ya karɓe rawaninka.
12 Me dadaurata, I pan wiaki i ur eu nan tanpaj en ai Kot, o a jolar pan pedoi jan kokolata. I pan intin po a mar en ai Kot, o ad en kanim en ai Kot, Ierujalem kap, me peidido jan ai Kot nanlan o mar ai kap.
Duk wanda ya ci nasara zan mai da shi ginshiƙi a haikalin Allahna. Ba kuwa zai sāke barin wurin ba. Zan rubuta a kansa sunan Allahna da kuma sunan birnin Allahna, sabuwar Urushalima, wadda take saukowa daga sama daga Allahna; ni kuma zan rubuta a kansa sabon sunana.
13 Me jalon a mia, en ron, me Nen o majani on momodijou kan!
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
14 Intin won tounlan en momodijou en Laodijea: let majan en me maraneki Amen, me jaunkadede lelapok melel, me tapin dodok en Kot.
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Lawodiseya, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomina Amin, amintaccen mashaidi mai gaskiya, da kuma mai mulkin halittar Allah.
15 I aja om wiawia kan, koe jota karakar o pil jota lamelamur. i men, koe en lamelamur de karakar!
Na san ayyukanka, ba ka da sanyi ba ka kuma da zafi. Na so da kai ɗaya ne daga ciki, ko sanyi, ko zafi!
16 Ari, koe me lou, a kaidin karakar de lamelamur, I ap pan muj kin uk wei jan nan au ai.
Amma domin kana tsaka-tsaka ba zafi ba, ba kuma sanyi ba, ina dab da tofar da kai daga bakina.
17 Pwe koe inda: Nai kapwapwa, i anekier kapwa kan, o i jota kin anane meakot, ap jaja, me koe jakanekan, o jo konekon, o jamama, o majkun, o kilijo.
Ka ce, ‘Ina da arziki; na sami dukiya ba na kuma bukatar kome.’ Amma ba ka gane ba cewa kai matsiyaci ne, abin tausayi, matalauci, makaho kana kuma tsirara.
18 I panaui uk, koe en neti jan ia kold linan, aki kijiniai, pwe koe en kapwapwala, o likau puetepuet, pwe koe en likauie uk, o kanamenok pan om kilijo der janjal, o wini en maj o, men elieliki maj om, en kilan waja.
Na shawarce ka ka sayi zinariyar da aka tace cikin wuta daga gare ni, don ka yi arziki; da fararen tufafi ka sa, don ka rufe kunyar tsirancinka; da kuma maganin ido ka sa a idanunka, don ka gani.
19 I kin kapun on o kaloke karoj, me I pokepoke. Koe nantion kaula!
Waɗanda nake ƙauna su nake tsawata wa, nake kuma horo. Saboda haka ka yi himma ka tuba.
20 Kilan, I kin u pan wanim o letelet. Meamen pan ron nil ai, ap ritinida wanim o, I pan pedelon re a, ap ian i mot on raj jaraui, o a ian ia.
Ga ni! Ina tsaye a bakin ƙofa, ina ƙwanƙwasawa. Duk wanda ya ji muryata ya kuma buɗe ƙofar, zan shiga in kuma ci tare da shi, shi kuma tare da ni.
21 Me dadaurata, I pan ki on i, en ian, ia mondi pon mol ai, dueta nai pil dadaurata, ap ian Jam ai mondi pon mol a.
Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon zama tare da ni a kursiyina, kamar yadda na ci nasara, kuma ina zaune tare da Ubana a kursiyinsa.
22 Me jalon a mia, i en ron, me Nen o majani on momodijou kan!
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.”

< Kaudial 3 >