< Lukaj 5 >

1 A KADEKADEO ni en aramaj toto ar tana don imp a, pwen roneron majan en Kot, a kotikot pon kailan le en Kalilaa,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Ap majani kijin jop riapot, me peipei nan le o, a jaujed akai keredi janer widen ar uk kai.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 I ari kotida pon apot ren jop oko, war en Jimon, kotin poeki re a, en kaiieila ekij jan ni jap o. I ari kaipokedi, kawewe on aramaj jan nan jop o.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 I lao kaimwijokela a majan, ap majani on Jimon: Jeijei kowei waja lol, ap kaduedi oma uk kan, pwe koma en jaikidi.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 A Jimon japen potoan on i: Main, je laiter pon lao lei waja ran, ap jota jaik at, ari jo ar majan, me i pan kaduekidi uk en.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Irail lao wiadar met, rap oro pena mam toto; ara uk ari ola.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Irail ari olole kij arail oko, me mi nin apot jop, pwe re en kodo jauaja irail. Irail ari kodo, kadirela jop riapot, ira ari pan mauidi.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Jimon Petruj lao kilaner mepukat, ap poridi jan Iejuj, potoan on: Main, re kotiwei jan ia, pwe aramaj jued amen nai.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Pwe a puriamuiki o ir karoj, me ian i, pweki jaik ar, me re jaikidi.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 A pil dueta Iakopuj o Ioanej nain Jepedauj ol oko, me ian Jimon. Iejuj ap kotin majani on Jimon: Koe der majak, pwe jan anjau wet kokola koe pan jaikidi aramaj.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Irail kaikilon on liman jap ar jop oko, re ap kajela karoj, idauendo i.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Kadekadeo ni a kotikot nan eu kanim, kilan, ol amen mia, me dir en tuketuk. A lao kilaner Iejuj, ap pupekidi maj a, poeki re a potoan on: Main, ma re kotin kupura, re pan kak on kamakel ia da.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 I ari kotin kapawei lim a jair i majani: I men, koe en makelekel. Ari, a tuketuk ma dan modi jan.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 I ari kotin inapwiedi i, der indan meamen; a kola kajale on pein uk jamero ko, o kida mairon, pweki om makelekeladar, me Mojej majanier, pwen kadede on irail.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 A a madan indand jili o po kon kalaimun pokon pena, pwen ron i o kelailada janar jomau kan
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 I ari kotin kelepela nan jap tan, pwen laolao.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Kadekadeo eu ran ni a kotin kaukaweweda, Parijilr o jaunkawewe kan, me mod imp a, irail pwarado jan kanim en Kalilaa o Iudaa karoj o jan Ierujalem; a rojon en Kaun o pwili wei jan i, kakelada amen amen.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 A kilan, ol akai roado aramaj amen me kokon madak, rap raparapaki duen ar pan kak walan lole, pwilikidi mo a.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 A ni ar jota kak diar waja, me re pan kai don impa pweki pokon o, rap dauda pon im o, kakiridi i nan oj ianaki pet, lao nan pun arail mon Iejuj.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 A lao mani arail pojon, ap kotin majani: Aramaj o, dip om akan lapwa jan uk er.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 A jaunkawewe o Pari jar akan ap monemoneloleki indada: Ij men et, me kin lalaue? Ij me kak lapwada dip akan, pwe Kot eta?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 A Iejuj lao mani ar monemonelol, ap kotin japen majani on irail: Da me komail kin monemoneloleki lol omail?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Da me monai ren inda, dip om akan lapwa jan uk er, de inda, uda, aluwei?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 A pwe komail en aja, me Nain aramaj manaman on lapada dip akan nin jappa, iei me a kotin majanieki on me kokon madak: I indai on uk, uda, aleki om kola deu om!
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 A madan uda mo’rail, kida a pet, me a wonon poa, koieilan im a kapikapina Kot.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Ir karoj ap puriamui kida o kapikapina Kot, o direkila majak indada: Ran wet kitail kilaner me kapwuriamui mele
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Murin mepukat a kotila jan waja o, ap majani jaunopwei amen ede Lewi momod nan wajan nopwei, ap majan on i: Idauen ia do!
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 I ari kajela a meakaroj, uda, idauenla i.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Lewi ari wiada kamadip lapalap on i nan im a; a jaunopwei ape me toto, me ian i ni tepel.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 A Parijar o arail jaunkawewe kan lipaned on japwilim a tounpadak kan indada: Da me komail ianaki jaunopwei o me dipan akan mana o nim.
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Iejuj ap kotin japen majani on irail: Me kelail jota mau on jaunwini, pwe me jomau kan.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I kodon ekeker don kalula me dipan akan a kaidin me pun kan.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Irail ap potoan on i: Da me tounpadak en Ioanej akan kaijejol pan pak toto o re kapakap toto, o pil dueta en Parijar akan, a japwilim omui kan kin tunole o nim?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 A Iejuj kotin majani on irail: O komail jota kak ki on toun kapar en kamadip en kapapaud en kaijejol arain ol kamod mi re’rail!
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 A eu ran ol kamod pan peuka wei jan irail, i ran oko re ap pan kaijejol.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 A kotin majani on irail karajeraj eu: Jota me kin deik on likau kap ni likau marin; a ma ei, a pan ter pajan likau kap; a kijan likau kap pil jota pan paroki on likau marin.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 A jota me kin kodie on wain kap nan ed marin; a ma ei, wain kap pan ter pajan ed akan, ap wudokila o ed akan pan ola.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 A re kin kodie on wain kap nan ed kap, ira karoj ap nekinek mau.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 O jota, me kin nim jan wain marin, pan mauki wain kap, pwe a kin inda: Me marin o me mau jan.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Lukaj 5 >