< Kaudial 16 >

1 O I ronger ngil laud eu sang nan im en kaudok o, mamasani ong tounlang isimen: Komail kowei, wudokedi ong sappa dal isu, me audekier ongiong en Kot.
Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
2 Men mas ap kotiwei wudokila ong sappa a dal, ap wiala kins sued ong aramas akan, me kilelekidi kilel en man o, o me pongi a kilel.
Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
3 O kariamen wudokila a dal ong nan madau ap wiala nta due nt’ en melar amen, ari me maur karos nan madau ap melar.
Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
4 O kasilimen wudokila a dal pon pilap o utun pil akan, rap ntalar.
Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
5 I ronger tounlang en pil akan masani: Komui me pung, me kotikot, o me kotikot mas, me saraui, pwe komui kadeikada due met.
Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
6 Pwe irail kieledier ntan me saraui o saukop akan, ari, kom kotin katungole kin ir nta; ari, me mau ong irail.
gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
7 I ronger me pei saraui o masani: Ei, Maing Kot, Kaun en meakaros, melel o me pung omui kadeik kan.
Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
8 A kapamen wudokila a dal pon katipin, a kapi ong i, en isiki kisiniai aramas akan.
Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
9 Ari, aramas rongkila karakar kaualap, o re lalaue mar en Kot, me Kaun pan kamekam pukat; a re sota kalukila, pwen wauneki i.
Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
10 O tounlang kalimen wudokila a dal pon mol en man o; ari a wei rotorotala; o re ke pasang lo arail pweki motakan madak.
Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
11 O irail lalaue Kot en lang, aki ar madak o ar kins akan, o re sota kalukila ar wiawia kan.
suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
12 O tounlang kawonemen wudokila a dal pon pilap Oiprat, a pil ap ngalengaledi, pwen kaonopada al mon nanmarki, me kotido sang ni pali mas en lang.
Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
13 O i kilanger, me sang nan au en drake, o sang nan au en man o, o sang nan au en saukop likam ngen samin silu dueta pros kai koda sang.
Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
14 Ir ngen en tewil kai, wiawia kilel kai, me kin pwaralang nanmarki en sappa kan, en kapokon ir penang mauin en ran lapalap en Kot manaman.
Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
15 Kilang, I pwarado dueta lipirap amen; meid pai, me kin masamasan, nekinekid a likau kan, pwe a de kilisola, rap kilang a kanamenok.
“Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
16 O re kapokon ir penang wasa, me ad a ni lokaia en Ipru Armakedon.
Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
17 O tounlang kaisimen wudokila a dal nin wäwä, ngil laud ap pwaradar sang im en kaudok nanlang, sang ni mol o mamasani: A wiauier.
Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
18 Ari, liol o ngil kai o nansapwe wiauier, o sappa rerer kaualap, sota due sang tapin aramas mi sappa, pwe me lapalap o mulatok.
Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
19 Ari, kanim lapalap pal pasang wiala silekis silu, o kanim en sap akan rongk pasang, o Kot kotin tamanda kanim Papilon, pwen kotiki ong i dal en wain en a ongiong lapalap.
Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
20 O dake karos mokid wei sang o nana kan solar sansal.
Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
21 O akel lapalap, toutouki paun epuki, me moredi sang lang lel aramas akan, o aramas lalaue Kot pweki kamekam akel, pwe iei kamekam me lapalapia.
Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.

< Kaudial 16 >