< Lukas 1 >

1 MURIN me toto ar intingiedier kasoi pan meakan, me kitail kin kamelele,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Duen ir, me kasokasoi ong kit, me saunkakede o papa pan masan sang ni tapi o,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 I ap pil lamedar, me mau, i en inting wong komui, Maing Tiopilus, pwe i lelepokki karos sang ni tapi o kokodo.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Pwe komui en asa duen meakan me komui aleer, me pung melel.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Ni muein Erodes nanmarki en Iudäa, samero amen mia, kisan pwin ong Apia, me mar a Sakarias, o a paud amen sang nain Aron seripein oko, me mar a Elisapet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ira karos me pung mon Kot, o ira ineneweita ni en Kaun a kusoned o tiak kan karos.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 A sota naira seri, pwe Elisapet li dapwan amen, o ira karos likailapalar.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 A kadekadeo ni a kapwaiada a dodok en samero mon Kot ni ansau o, me a pwin pwaisaneki,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Duen a kin wiaui ren samero kan, o ansau en isik mairong lao leler, a kotilong ong nan im en kaudok en Kaun o.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 A pokon kalaimun mi liki, wiawia kapakap ni klok en isis.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 A tounlang en Kaun amen pwara dong i, kotikot ni pali maun en pei saraui en potik.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Sakarias lao masani, ap lusikida o masapwekada.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 A tounlang o masani ong i: Sakarias, der masak, pwe om kapakap pwaidar, om paud Elisapet pan naitikeda seri ol amen, a koe pan ki ong mar a Ioanes.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 O a pan kare ong uk peren o popol, o me toto pan perenki a ipwidi.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Pwe a pan lapalap ren Kaun o, a sota pan nim wain, pil so eu song en soko; a pan dir en Ngen saraui nan kupur en in a.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 A me toto ren nain Israel akan, me a pan kawuki ong Kaun ar Kot.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 A pan tiong mo a ni ngen o roson en Elias, pwen kawuki ong seri kan mongiong en sam arail akan o me sopeik kan ong lamalam en me pung kan, pwen kaonopadang Kaun o pwin aramas lelapok eu.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 A Sakarias masani ong tounlang o: Da me i en asaki me wet? Pwe i ol laudalar amen, o ai paud pil likailapalar.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 A tounlang sapeng masani ong i: Ngai Kapriel, me kin ariri Kot, o me pakadarado, en lokaia ong uk, o wa dong uk rongamau pukat.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Kilang, koe pan lotong la, o sasa lokaia lao lel ran o, me mepukat pan pwaida, pweki om sota kamelele ai kasoi, me pan pwaida ni a ansau.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 A pokon o auiaui Sakarias, puriamuiki a pwapwand nan im en kaudok.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 A lao pedoi sang, a solar kak masan ong irail. Irail ap dedeki, me a udial manaman eu nan im en kaudok o. A olol ong irail o lotonglar.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Kadekadeo ran akan en a dodok lao nikier, a kotin purelang sap we koieilang im a.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Murin ran pukat a paud Elisapet liseanda o mimieta nan deu a saunipong limau indada:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Iduen Kaun o kotin wiai ong ia ni ran oko, ni a kotin masan dong ia, pwen kotiki sang ia kanamenok pai ren aramas.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Ni kawonu en saunipong tounlang Kapriel pakadarala sang ren Kot ong nan kanim en Kaliläa eu, me ad a Nasaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Ren seripein makelekel amen, me kisin nin ong ol amen, me mar a Iosep, kisan kadaudok en Dawid; seripein makelekel o adaneki Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Tounlang o kotilong ong nan deu a masani ong i: Kaselelia Maing, kom meid pai, Kaun o kotikot re omui! Kom meid pai nan pung en li akan!
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 A lao kilanger i, o rongadar a masan, ap masapwekadar madamadaua: Duen song en ranamau o.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 A tounlang masani ong i: Maria, ender masak, pwe komui me konekonelar ren Kot.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 A kilang, komui pan liseanda o naitikeda seri ol amen, a komui pan ki ong mar a Iesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Nan i me pan lapalap, o a pan maraneki Sapwilim en Kaun lapalap, o Kaun Kot pan kotiki ong i mol en sam a Dawid.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 O a pan kakaunda kadaudok en Iakop kokolata, o sapwilim a wei sota pan imwila. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Maria ap masani ong tounlang o: Daduen mepukat pan kak wiaui, aki i sasa ol amen?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Tounlang o kotin sapeng masani ong i: Ngen saraui pan kotin ti po omui o roson en Kaun lapalap pan kipa komui di, i me saraui o, me pan ipwi sang komui, pan maraneki: Sapwilim en Kot.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 O masani, ri om Elisapet pil liseandar ni a likailapala, a pan naitikeda seri ol amen, a kawonu en saunipong ansau wet; iei i me dapwan,
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Pwe sota meakot, me Kot sota kak ong.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 A Maria potoan ong: Masani, ngai lidu en Kaun o; en wiaui ong ia duen omui masan. Tounlang o ap kotila sang re a.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 I ran oko Maria madang kotila pon nana o nan kanim en Iuda eu,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Ap pedelong ong nan im en Sakarias o ranamau ong Elisapet.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Kadekadeo Elisapet lao ronger en Maria a ranamau ong i, seri o ap mokideda nan kaped a; a Elisapet ap direkila Ngen saraui,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 O ngil laudeda masani: Komui meid pai ren li akan, o meid iasanai ipwin kupur omui!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 A iaduen pai wet a ko sang ia, pwe in en ai Kaun koti dong ia?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Masani, ni ai ronger omui ranamau, seri o ap mokideda nan kaped i aki a peren.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 O komui meid pai, pweki komui poson! Pwe a pan pwaida, me Kaun o kotin masani ong komui.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Maria ap masani: Lol ai kapinga Kaun o,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 O ngen i perenki Kot ai Saunkamaur.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Pwe a kotin kupurala sapwilim a lidu tikitik o. Kilang, sang met o kokolata di karos pan kapai kin ia,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Pwe a kotin wiaer song en manaman ong ia, me lapalap o mar a me saraui.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 A kotin kalangan ong di karos kokolata, ong irail me kin lan i.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 O a kotin wia kida lim a manaman akan. O a kotin karawan pasang, me kin lemai nan mongiong arail.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 A kotin sikin wei saupeidi kan sang mol ar, ap id kasapwilada me tikitik kan.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 A kotin kamede kida kapwa me men mangadar akan, ap kotin kadarala kaip me kapwapwa kan.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 A kotin upor kin sapwilim a ladu Israel, o kotin tamataman a kalangan,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Duen a kotin masani ong sam atail akan, ong Apraam o kadaudok a kokolata. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 A Maria kotikot re a saunipong silu, ap purelang im a.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Ari, ansaun Elisapet leler pwen naitik, a naitikeda seri ol amen.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 O men imp a kan o sau i rongadar, me Kaun o kotin kupura i, rap iang i peren kida.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Kadekadeo auel en ran o re pwara dong sirkomsais seri o; ir ari ki ong mar en sam a Sakarias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 A in a sapeng indada: O kaidin, pwe a pan maraneki Ioanes.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Irail ap indang i: Nan sota sau om men me maraneki met.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Irail ap olol ong sam a, duen me a mauki, seri en adaneki.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 I ari poeki slet eu, ap intingiedier o masani: A pan adaneki Ioanes. Irail karos ap puriamuiki.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 A madang silang i wasok pasang o tenap a sapadokada; i ari masani o kapinga Kot.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 A masak kipadi karos, me kaukauson imp ar, o wiawia pukat lolok sili pon nana en Iudäa karos.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 A karos me rongadar, kin nekinekid nan mongiong arail, indada: Da me seri men et pan wiala? Pwe lim en Kaun o kotin iang i.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 A sam a Sakarias direkila Ngen saraui ap kokopada masani:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Kapinga ong Kaun Kot en Israel, pwe a kotidier ren sapwilim a aramas akan dore ir ala.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 O kotin wiadang kitail kamaur patail sang nan kadaudok en sapwilim a ladu Dawid.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Duen a kotin masanier ren sapwilim a saukop saraui kan, sang tapin kaua kokodo, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Me a pan kotin dore kitail la sang ren atail imwintiti o sang nan pa en me kailong kin kitail,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 O kotin kalangan ong sam atail akan, o kotin kupureda a inau saraui,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 O kaula eu, me a kotin kauki ong sam atail Apraam, en kotiki ong kitail.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Pwe sen dore sang nan pa en atail imwintiti, ap papa i so masak,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Nin tiak lelapok o pung mon silang i ran karos kokolata.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 A koe nai seri pan adaneki: Saukop en me lapalap o, pwe koe pan tiong mon silang en Kaun o, pwen kaonopada sapwilim a al akan.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Pwen kawewe ong sapwilim a aramas kamaur, iei lapwa pan dip ar akan;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Pweki en atail Kot a kalangan melel, me marain dakaraki dong kitail sang poa.
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Pwen kamaraini toun pali rotorot o mot en mela, o kainen ong nä atail nan al en popol.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 A seri o kakairida, o kelail ni ngen e, o a kin mimi nan sap tan, lao a pan sansal ong Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lukas 1 >