< روت 4 >

بوعز به دروازهٔ شهر که محل اجتماع مردم شهر بود رفت و در آنجا نشست. آنگاه آن مرد که نزدیکترین خویشاوند شوهر نعومی بود به آنجا آمد. بوعز او را صدا زده گفت: «بیا اینجا! می‌خواهم چند کلمه‌ای با تو صحبت کنم.» او آمد و نزد بوعز نشست. 1
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
آنگاه بوعز ده نفر از ریش‌سفیدان شهر را دعوت کرد تا شاهد باشند. 2
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
بوعز به خویشاوند خود گفت: «تو می‌دانی که نعومی از سرزمین موآب برگشته است. او در نظر دارد ملک برادرمان الیملک را بفروشد. 3
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
فکر کردم بهتر است در این باره با تو صحبت کنم تا اگر مایل باشی، در حضور این جمع آن را خریداری نمایی. اگر خریدار آن هستی همین حالا بگو. در غیر این صورت خودم آن را می‌خرم. اما تو بر من مقدم هستی و بعد از تو حق من است که آن ملک را خریداری نمایم.» آن مرد جواب داد: «بسیار خوب، من آن را می‌خرم.» 4
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
بوعز به او گفت: «تو که زمین را می‌خری موظف هستی با روت نیز ازدواج کنی تا بچه‌دار شود و فرزندانش وارث آن زمین گردند و به این وسیله نام شوهرش زنده بماند.» 5
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
آن مرد گفت: «در این صورت من از حق خرید زمین می‌گذرم، زیرا فرزند روت وارث ملک من نیز خواهد بود. تو آن را خریداری کن.» 6
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
(در آن روزگار در اسرائیل مرسوم بود که هرگاه شخصی می‌خواست حق خرید ملکی را به دیگری واگذار کند، کفشش را از پا درمی‌آورد و به او می‌داد. این عمل، معامله را در نظر مردم معتبر می‌ساخت.) 7
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
پس آن مرد وقتی به بوعز گفت: «تو آن زمین را خریداری کن»، کفشش را از پا درآورد و به او داد. 8
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
آنگاه بوعز به ریش‌سفیدان محل و مردمی که در آنجا ایستاده بودند گفت: «شما شاهد باشید که امروز من تمام املاک الیملک، کلیون و محلون را از نعومی خریدم. 9
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
در ضمن با روت موآبی، زن بیوهٔ محلون ازدواج خواهم کرد تا او پسری بیاورد که وارث شوهر مرحومش گردد و به این وسیله نام او در خاندان و در زادگاهش زنده بماند.» 10
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
همهٔ مشایخ و مردمی که در آنجا بودند گفتند: «ما شاهد بر این معامله هستیم. خداوند این زنی را که به خانهٔ تو خواهد آمد، مانند راحیل و لیه بسازد که با هم دودمان اسرائیل را بنا کردند. باشد که تو در افراته و بیت‌لحم معروف و کامیاب شوی. 11
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
با فرزندانی که خداوند به وسیلۀ این زن به تو می‌بخشد، خاندان تو مانند خاندان فارَص پسر تامار و یهودا باشد.» 12
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
پس بوعز با روت ازدواج کرد و خداوند به آنها پسری بخشید. 13
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
زنان شهر بیت‌لحم به نعومی گفتند: «سپاس بر خداوند که تو را بی‌سرپرست نگذاشت و نوه‌ای به تو بخشید. باشد که او در اسرائیل معروف شود. 14
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
عروست که تو را دوست می‌دارد و برای تو از هفت پسر بهتر بوده، پسری به دنیا آورده است. این پسر جان تو را تازه خواهد کرد و در هنگام پیری از تو مراقبت خواهد نمود.» 15
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
نعومی نوزاد را در آغوش گرفت و دایهٔ او شد. 16
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
زنان همسایه آن نوزاد را عوبید نامیده گفتند: «پسری برای نعومی متولد شد!» (عوبید پدر یَسا و پدر بزرگ داوود پادشاه است.) 17
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
این است نسب نامهٔ بوعز که از فارص شروع شده، به داوود ختم می‌شود: فارص، حصرون، رام، عمیناداب، نحشون، سلمون، بوعز، عوبید، یَسا و داوود. 18
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< روت 4 >