< زکریا 8 >

و کلام یهوه صبایوت بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
«یهوه صبایوت چنین می‌فرماید: برای صهیون غیرت عظیمی دارم و با غضب سخت برایش غیور هستم. ۲ 2
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
خداوند چنین می‌گوید: به صهیون مراجعت نموده‌ام و در میان اورشلیم ساکن خواهم شد و اورشلیم به شهر حق و کوه یهوه صبایوت به کوه مقدس مسمی خواهدشد. ۳ 3
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: مردان پیر وزنان پیر باز در کوچه های اورشلیم خواهندنشست و هر یکی از ایشان به‌سبب زیادتی عمرعصای خود را در دست خود خواهد داشت. ۴ 4
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
وکوچه های شهر از پسران و دختران که درکوچه هایش بازی می‌کنند پر خواهد شد. ۵ 5
Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: اگر این امر در این‌روزها به نظر بقیه این قوم عجیب نماید آیا در نظر من عجیب خواهد نمود؟ قول یهوه صبایوت این است. ۶ 6
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
«یهوه صبایوت چنین می‌گوید: اینک من قوم خود را از زمین مشرق و از زمین مغرب آفتاب خواهم رهانید. ۷ 7
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
و ایشان را خواهم آورد که دراورشلیم سکونت نمایند و ایشان قوم من خواهندبود و من براستی و عدالت خدای ایشان خواهم بود. ۸ 8
Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: دستهای شما قوی شود‌ای کسانی که در این ایام این کلام را از زبان انبیا شنیدید که آن در روزی که بنیادخانه یهوه صبایوت را برای بنا نمودن هیکل نهادند واقع شد. ۹ 9
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
زیرا قبل از این ایام مزدی برای انسان نبود و نه مزدی به جهت حیوان؛ و به‌سبب دشمن برای هر‌که خروج و دخول می‌کردهیچ سلامتی نبود و من همه کسان را به ضدیکدیگر واداشتم. ۱۰ 10
Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
اما الان یهوه صبایوت می‌گوید: من برای بقیه این قوم مثل ایام سابق نخواهم بود. ۱۱ 11
Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
زیرا که زرع سلامتی خواهد بودو مو میوه خود را خواهد داد و زمین محصول خود را خواهد آورد و آسمان شبنم خویش راخواهد بخشید و من بقیه این قوم را مالک جمیع این چیزها خواهم گردانید. ۱۲ 12
“Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
و واقع خواهد شد چنانکه شما‌ای خاندان یهودا وای خاندان اسرائیل در میان امت‌ها (مورد)لعنت شده‌اید، همچنان شما را نجات خواهم داد تا (مورد) برکت بشوید؛ پس مترسید ودستهای شما قوی باشد. ۱۳ 13
Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
زیرا که یهوه صبایوت چنین می‌گوید: چنانکه قصد نمودم که به شما بدی برسانم حینی که پدران شماخشم مرا به هیجان آوردند و یهوه صبایوت می‌گوید که از آن پشیمان نشدم. ۱۴ 14
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
همچنین در این‌روزها رجوع نموده، قصد خواهم نمود که به اورشلیم و خاندان یهودا احسان نمایم. پس ترسان مباشید. ۱۵ 15
kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
و این است کارهایی که بایدبکنید: با یکدیگر راست گویید و در دروازه های خود انصاف و داوری سلامتی را اجرا دارید. ۱۶ 16
Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
و در دلهای خود برای یکدیگر بدی میندیشید و قسم دروغ را دوست مدارید، زیراخداوند می‌گوید از همه این کارها نفرت دارم.» ۱۷ 17
kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
و کلام یهوه صبایوت بر من نازل شده، گفت: ۱۸ 18
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
«یهوه صبایوت چنین می‌گوید: روزه ماه چهارم و روزه ماه پنجم و روزه ماه هفتم و روزه ماه دهم برای خاندان یهودا به شادمانی و سرور وعیدهای خوش مبدل خواهد شد پس راستی وسلامتی را دوست بدارید. ۱۹ 19
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: بار دیگر واقع خواهد شد که قوم‌ها و ساکنان شهرهای بسیار خواهند آمد. ۲۰ 20
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
و ساکنان یک شهر به شهر دیگر رفته، خواهندگفت: بیایید برویم تا از خداوند مسالت نماییم ویهوه صبایوت را بطلبیم و من نیز خواهم آمد. ۲۱ 21
mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
و قوم های بسیار و امت های عظیم خواهندآمد تا یهوه صبایوت را در اورشلیم بطلبند و ازخداوند مسالت نمایند. ۲۲ 22
Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید در آن روزها ده نفر از همه زبانهای امت‌ها به دامن شخص یهودی چنگ زده، متمسک خواهند شد و خواهند گفت همراه شما می‌آییم زیرا شنیده‌ایم که خدا با شمااست.» ۲۳ 23
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”

< زکریا 8 >