< مکاشفهٔ یوحنا 15 >

و علامت دیگر عظیم و عجیبی درآسمان دیدم، یعنی هفت فرشته‌ای که هفت بلایی دارند که آخرین هستند، زیرا که به آنها غضب الهی به انجام رسیده است. ۱ 1
Na ga wata babbar alama mai banmamaki a sama, mala’iku bakwai da annobai bakwai na ƙarshe, na ƙarshe, domin da su ne fushin Allah ya cika.
و دیدم مثال دریایی از شیشه مخلوط به آتش و کسانی راکه بر وحش و صورت او و عدد اسم او غلبه می یابند، بر دریای شیشه ایستاده و بربطهای خدارا بدست گرفته، ۲ 2
Sai na ga abin da ya yi kamar tekun gilashi gauraye da wuta kuma tsaye kusa da teku, waɗanda suka ci nasara bisan dabbar da siffarta da bisan lambar sunanta. Suna riƙe da garayu waɗanda Allah ya ba su
سرود موسی بنده خدا و سرودبره را می‌خوانند و می‌گویند: «عظیم و عجیب است اعمال تو‌ای خداوند خدای قادر مطلق! عدل و حق است راههای تو‌ای پادشاه امت‌ها. ۳ 3
suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
کیست که از تو نترسد، خداوندا و کیست که نام تو را تمجید ننماید؟ زیرا که تو تنها قدوس هستی و جمیع امت‌ها آمده، در حضور توپرستش خواهند کرد، زیرا که احکام تو ظاهرگردیده است. ۴ 4
Wane ne ba zai ji tsoronka, yă kuma kawo ɗaukaka ga sunanka ba, ya Ubangiji? Gama kai kaɗai ne mai tsarki. Dukan al’ummai za su zo su yi sujada a gabanka, gama an bayyana ayyukan adalcinka.”
و بعد از این دیدم که قدس خیمه شهادت درآسمان گشوده شد، ۵ 5
Bayan wannan sai na duba, a cikin sama kuwa sai ga haikali, wato, tabanakul na Shaida, a buɗe.
و هفت فرشته‌ای که هفت بلا داشتند، کتانی پاک و روشن دربر کرده و کمرایشان به کمربند زرین بسته، بیرون آمدند. ۶ 6
Daga cikin haikalin mala’iku bakwai tare da annobai bakwai suka fito. Suna saye da tufafin lilin masu tsabta masu walƙiya, suna kuma saye da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.
ویکی از آن چهار حیوان، به آن هفت فرشته، هفت پیاله زرین داد، پر از غضب خدا که تا ابدالاباد زنده است. (aiōn g165) ۷ 7
Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn g165)
و قدس از جلال خدا و قوت او پر دودگردید. و تا هفت بلای آن هفت فرشته به انجام نرسید، هیچ‌کس نتوانست به قدس درآید. ۸ 8
Aka kuma cika haikalin da hayaƙi daga ɗaukakar Allah da kuma daga ikonsa, kuma ba wanda ya iya shiga haikalin sai da aka cika annobai bakwai nan na mala’iku bakwai.

< مکاشفهٔ یوحنا 15 >