< مزامیر 66 >
برای سالار مغنیان. سرود و مزمور ای تمامی زمین، برای خدا بانگ شادمانی بزنید! | ۱ 1 |
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
جلال نام او رابسرایید! و در تسبیح او جلال او را توصیف نمایید! | ۲ 2 |
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
خدا را گویید: «چه مهیب است کارهای تو! از شدت قوت تو دشمنانت نزد تو تذلل خواهند کرد! | ۳ 3 |
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
تمامی زمین تو را پرستش خواهند کرد و تو را خواهند سرایید و به نام توترنم خواهند نمود.» سلاه. | ۴ 4 |
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
بیایید کارهای خدا را مشاهده کنید. او درکارهای خود به بنی آدم مهیب است. | ۵ 5 |
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
دریا را به خشکی مبدل ساخت و مردم از نهر با پا عبورکردند. در آنجا بدو شادی نمودیم. | ۶ 6 |
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
در توانایی خود تا به ابد سلطنت میکند و چشمانش مراقب امتها است. فتنه انگیزان خویشتن را برنیفرازند، سلاه. | ۷ 7 |
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
ای قومها، خدای ما را متبارک خوانید وآواز تسبیح او را بشنوانید. | ۸ 8 |
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
که جانهای ما را درحیات قرار میدهد و نمی گذارد که پایهای مالغزش خورد. | ۹ 9 |
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
زیراای خدا تو ما را امتحان کردهای و ما را غال گذاشتهای چنانکه نقره راغال میگذارند. | ۱۰ 10 |
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
ما را به دام درآوردی و باری گران بر پشتهای ما نهادی. | ۱۱ 11 |
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
مردمان را بر سرما سوار گردانیدی و به آتش و آب درآمدیم. پس ما را بهجای خرم بیرون آوردی. | ۱۲ 12 |
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
قربانی های سوختنی به خانه تو خواهم آورد. نذرهای خود را به تو وفا خواهم نمود، | ۱۳ 13 |
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
که لبهای خود را بر آنها گشودم و در زمان تنگی خودآنها را به زبان خود آوردم. | ۱۴ 14 |
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
قربانی های سوختنی پرواری را نزد تو خواهم گذرانید. گوسالهها و بزها را با بخور قوچها ذبح خواهم کرد، سلاه. | ۱۵ 15 |
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
ای همه خداترسان بیایید و بشنوید تا ازآنچه او برای جان من کرده است خبر دهم. | ۱۶ 16 |
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
به دهانم نزد او آواز خود را بلند کردم و تسبیح بلند بر زبان من بود. | ۱۷ 17 |
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
اگر بدی را در دل خودمنظور میداشتم، خداوند مرا نمی شنید. | ۱۸ 18 |
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
لیکن خدا مرا شنیده است و به آواز دعای من توجه فرموده. | ۱۹ 19 |
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
متبارک باد خدا که دعای مرا ازخود، و رحمت خویش را از من برنگردانیده است. | ۲۰ 20 |
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!