< مزامیر 44 >

برای سالار مغنیان. قصیده بنی قورح ای خدا به گوشهای خود شنیده‌ایم وپدران ما، ما را خبر داده‌اند، از کاری که در روزهای ایشان و در ایام سلف کرده‌ای. ۱ 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
تو به‌دست خود امت‌ها را بیرون کردی، اماایشان را غرس نمودی. قومها را تباه کردی، اما ایشان را منتشر ساختی. ۲ 2
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
زیرا که به شمشیر خود زمین را تسخیر نکردند و بازوی ایشان ایشان را نجات نداد. بلکه دست راست تو وبازو و نور روی تو. زیرا از ایشان خرسندبودی. ۳ 3
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
‌ای خدا تو پادشاه من هستی. پس برنجات یعقوب امر فرما. ۴ 4
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
به مدد تو دشمنان خود راخواهیم افکند و به نام تو مخالفان خویش راپایمال خواهیم ساخت. ۵ 5
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
زیرا بر کمان خودتوکل نخواهم داشت و شمشیرم مرا خلاصی نخواهد داد. ۶ 6
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
بلکه تو ما را از دشمنان ما خلاصی دادی و مبغضان ما را خجل ساختی. ۷ 7
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
تمامی روزبر خدا فخر خواهیم کرد و نام تو را تا به ابد تسبیح خواهیم خواند، سلاه. ۸ 8
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
لیکن الان تو ما را دورانداخته و رسوا ساخته‌ای و با لشکرهای ما بیرون نمی آیی. ۹ 9
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
و ما را از پیش دشمن روگردان ساخته‌ای و خصمان ما برای خویشتن تاراج می‌کنند. ۱۰ 10
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
ما را مثل گوسفندان برای خوراک تسلیم کرده‌ای و ما را در میان امت‌ها پراکنده ساخته‌ای. ۱۱ 11
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
قوم خود را بی‌بها فروختی و ازقیمت ایشان نفع نبردی. ۱۲ 12
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
ما را نزد همسایگان ماعار گردانیدی. اهانت و سخریه نزد آنانی که گرداگرد مایند. ۱۳ 13
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
ما را در میان امت هاضرب‌المثل ساخته‌ای. جنبانیدن سر در میان قوم‌ها. ۱۴ 14
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
و رسوایی من همه روزه در نظر من است. و خجالت رویم مرا پوشانیده است، ۱۵ 15
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
ازآواز ملامت گو و فحاش، از روی دشمن و انتقام گیرنده. ۱۶ 16
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
این همه بر ما واقع شد. اما تو را فراموش نکردیم و در عهد تو خیانت نورزیدیم. ۱۷ 17
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
دل مابه عقب برنگردید و پایهای ما از طریق تو انحراف نورزید. ۱۸ 18
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
هرچند ما را در مکان اژدرها کوبیدی و ما را به سایه موت پوشانیدی. ۱۹ 19
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
نام خدای خود را هرگز فراموش نکردیم و دست خود را به خدای غیر برنیفراشتیم. ۲۰ 20
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
آیا خدا این راغوررسی نخواهد کرد؟ زیرا او خفایای قلب رامی داند. ۲۱ 21
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
هر آینه به‌خاطر تو تمامی روز کشته می‌شویم و مثل گوسفندان ذبح شمرده می‌شویم. ۲۲ 22
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
‌ای خداوند بیدار شو چراخوابیده‌ای؟ برخیز و ما را تا به ابد دور مینداز. ۲۳ 23
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
چرا روی خود را پوشانیدی و ذلت و تنگی مارا فراموش کردی؟ ۲۴ 24
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
زیرا که جان ما به خاک خم شده است و شکم ما به زمین چسبیده. ۲۵ 25
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
به جهت اعانت ما برخیز و بخاطر رحمانیت خود ما رافدیه ده. ۲۶ 26
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< مزامیر 44 >