< لوقا 5 >

و هنگامی که گروهی بر وی ازدحام می نمودند تا کلام خدا را بشنوند، او به کناردریاچه جنیسارت ایستاده بود. ۱ 1
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
و دو زورق رادر کنار دریاچه ایستاده دید که صیادان از آنهابیرون آمده، دامهای خود را شست و شومی نمودند. ۲ 2
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
پس به یکی از آن دو زورق که مال شمعون بود سوار شده، از او درخواست نمود که از خشکی اندکی دور ببرد. پس در زورق نشسته، مردم را تعلیم می‌داد. ۳ 3
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
و چون از سخن‌گفتن فارغ شد، به شمعون گفت: «به میانه دریاچه بران و دامهای خود رابرای شکار بیندازید.» ۴ 4
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
شمعون در جواب وی گفت: «ای استاد، تمام شب را رنج برده چیزی نگرفتیم، لیکن به حکم تو، دام را خواهیم انداخت.» ۵ 5
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
و چون چنین کردند، مقداری کثیر ازماهی صید کردند، چنانکه نزدیک بود دام ایشان گسسته شود. ۶ 6
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
و به رفقای خود که در زورق دیگربودند اشاره کردند که آمده ایشان را امداد کنند. پس آمده هر دو زورق را پر کردند بقسمی که نزدیک بود غرق شوند. ۷ 7
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
شمعون پطرس چون این را بدید، بر پایهای عیسی افتاده، گفت: «ای خداوند از من دور شو زیرا مردی گناهکارم.» ۸ 8
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
چونکه به‌سبب صیدماهی که کرده بودند، دهشت بر او و همه رفقای وی مستولی شده بود. ۹ 9
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
و هم چنین نیز بریعقوب و یوحنا پسران زبدی که شریک شمعون بودند. عیسی به شمعون گفت: «مترس. پس از این مردم را صید خواهی کرد.» ۱۰ 10
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
پس چون زورقهارا به کنار آوردند همه را ترک کرده، از عقب اوروانه شدند. ۱۱ 11
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
و چون او در شهری از شهرها بود ناگاه مردی پر از برص آمده، چون عیسی را بدید، به روی در‌افتاد و از او درخواست کرده، گفت: «خداوندا، اگر خواهی می‌توانی مرا طاهرسازی.» ۱۲ 12
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
پس او دست آورده، وی را لمس نمود و گفت: «می‌خواهم. طاهر شو.» که فور برص از او زایل شد. ۱۳ 13
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
و او را قدغن کرد که «هیچ‌کس را خبر مده، بلکه رفته خود را به کاهن بنما و هدیه‌ای بجهت طهارت خود، بطوری که موسی فرموده است، بگذران تا بجهت ایشان شهادتی شود.» ۱۴ 14
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
لیکن خبر او بیشتر شهرت یافت و گروهی بسیار جمع شدند تا کلام او رابشنوند و از مرضهای خود شفا یابند، ۱۵ 15
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
و او به ویرانه‌ها عزلت جسته، به عبادت مشغول شد. ۱۶ 16
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
روزی از روزها واقع شد که او تعلیم می‌دادو فریسیان و فقها که از همه بلدان جلیل و یهودیه و اورشلیم آمده، نشسته بودند وقوت خداوندبرای شفای ایشان صادر می‌شد، ۱۷ 17
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
که ناگاه چندنفر شخصی مفلوج را بر بستری آوردند ومی خواستند او را داخل کنند تا پیش روی وی بگذارند. ۱۸ 18
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
و چون به‌سبب انبوهی مردم راهی نیافتند که او را به خانه درآورند بر پشت بام رفته، او را با تختش از میان سفالها در وسط پیش عیسی گذاردند. ۱۹ 19
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
چون او ایمان ایشان را دید، به وی گفت: «ای مرد، گناهان تو آمرزیده شد.» ۲۰ 20
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
آنگاه کاتبان و فریسیان در خاطر خود تفکرنموده، گفتن گرفتند: «این کیست که کفر می‌گوید. جز خدا و بس کیست که بتواند گناهان رابیامرزد؟» ۲۱ 21
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
عیسی افکار ایشان را درک نموده، در جواب ایشان گفت: «چرا در خاطر خود تفکرمی کنید؟ ۲۲ 22
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
کدام سهلتر است، گفتن اینکه گناهان تو آمرزیده شد، یا گفتن اینکه برخیز و بخرام؟ ۲۳ 23
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
لیکن تا بدانید که پسر انسان را استطاعت آمرزیدن گناهان بر روی زمین هست، مفلوج راگفت، تو را می‌گویم برخیز و بستر خود رابرداشته، به خانه خود برو.» ۲۴ 24
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
در ساعت برخاسته، پیش ایشان آنچه بر آن خوابیده بودبرداشت و به خانه خود خدا را حمدکنان روانه شد. ۲۵ 25
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
و حیرت همه را فرو گرفت و خدا راتمجید می‌نمودند و خوف بر ایشان مستولی شده، گفتند: «امروز چیزهای عجیب دیدیم.» ۲۶ 26
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
از آن پس بیرون رفته، باجگیری را که لاوی نام داشت، بر باجگاه نشسته دید. او را گفت: «از عقب من بیا.» ۲۷ 27
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
در حال همه‌چیز را ترک کرده، برخاست و در عقب وی روانه شد. ۲۸ 28
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
و لاوی ضیافتی بزرگ در خانه خود برای او کرد و جمعی بسیار از باجگیران و دیگران با ایشان نشستند. ۲۹ 29
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
اما کاتبان ایشان و فریسیان همهمه نموده، به شاگردان او گفتند: «برای چه با باجگیران وگناهکاران اکل و شرب می‌کنید؟» ۳۰ 30
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
عیسی درجواب ایشان گفت: «تندرستان احتیاج به طبیب ندارند بلکه مریضان. ۳۱ 31
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
و نیامده‌ام تا عادلان بلکه تا عاصیان را به توبه بخوانم.» ۳۲ 32
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
پس به وی گفتند: «از چه سبب شاگردان یحیی روزه بسیار می‌دارند و نماز می‌خوانند وهمچنین شاگردان فریسیان نیز، لیکن شاگردان تواکل و شرب می‌کنند.» ۳۳ 33
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
بدیشان گفت: «آیامی توانید پسران خانه عروسی را مادامی که دامادبا ایشان است روزه‌دار سازید؟ ۳۴ 34
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
بلکه ایامی می‌آید که داماد از ایشان گرفته شود، آنگاه در آن روزها روزه خواهند داشت.» ۳۵ 35
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
و مثلی برای ایشان آورد که «هیچ‌کس پارچه‌ای از جامه نو را بر جامه کهنه وصله نمی کند والا آن نو را پاره کند و وصله‌ای که از نوگرفته شد نیز در خور آن کهنه نبود. ۳۶ 36
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
و هیچ‌کس شراب نو را در مشکهای کهنه نمی ریزد والاشراب نو، مشکها را پاره می‌کند و خودش ریخته و مشکها تباه می‌گردد. ۳۷ 37
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
بلکه شراب نو را درمشکهای نو باید ریخت تا هر دو محفوظ بماند. ۳۸ 38
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
و کسی نیست که چون شراب کهنه را نوشیده فی الفور نو را طلب کند، زیرا می‌گوید کهنه بهتراست.» ۳۹ 39
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< لوقا 5 >