< لوقا 21 >

و نظر کرده دولتمندانی را دید که هدایای خود را در بیت‌المال می‌اندازند. ۱ 1
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
و بیوه‌زنی فقیر را دید که دو فلس در آنجا انداخت. ۲ 2
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
پس گفت: «هرآینه به شمامی گویم این بیوه فقیر از جمیع آنها بیشترانداخت. ۳ 3
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
زیرا که همه ایشان از زیادتی خود درهدایای خدا انداختند، لیکن این زن از احتیاج خود تمامی معیشت خویش را انداخت. ۴ 4
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
و چون بعضی ذکر هیکل می‌کردند که به سنگهای خوب و هدایا آراسته شده است گفت: ۵ 5
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
«ایامی می‌آید که از این چیزهایی که می‌بینید، سنگی بر سنگی گذارده نشود، مگر اینکه به زیرافکنده خواهد شد. ۶ 6
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
و از او سوال نموده، گفتند: «ای استاد پس این امور کی واقع می‌شود وعلامت نزدیک شدن این وقایع چیست؟» ۷ 7
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
گفت: «احتیاط کنید که گمراه نشوید. زیرا که بسا به نام من آمده خواهند گفت که من هستم و وقت نزدیک است. پس از عقب ایشان مروید. ۸ 8
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
و چون اخبارجنگها و فسادها را بشنوید، مضطرب مشویدزیرا که وقوع این امور اول ضرور است لیکن انتهادر ساعت نیست.» ۹ 9
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
پس به ایشان گفت: «قومی با قومی ومملکتی با مملکتی مقاومت خواهند کرد. ۱۰ 10
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
وزلزله های عظیم در جایها و قحطیها و وباها پدیدو چیزهای هولناک و علامات بزرگ از آسمان ظاهر خواهد شد. ۱۱ 11
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
و قبل از این همه، بر شمادست اندازی خواهند کرد و جفا نموده شما را به کنایس و زندانها خواهند سپرد و در حضورسلاطین و حکام بجهت نام من خواهند برد. ۱۲ 12
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
واین برای شما به شهادت خواهد انجامید. ۱۳ 13
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
پس در دلهای خود قرار دهید که برای حجت آوردن، پیشتر اندیشه نکنید، ۱۴ 14
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
زیرا که من به شما زبانی وحکمتی خواهم داد که همه دشمنان شما با آن مقاومت و مباحثه نتوانند نمود. ۱۵ 15
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
و شما راوالدین و برادران و خویشان و دوستان تسلیم خواهند کرد و بعضی از شما را به قتل خواهندرسانید. ۱۶ 16
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
و جمیع مردم به جهت نام من شما رانفرت خواهند کرد. ۱۷ 17
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
ولکن مویی از سر شما گم نخواهد شد. ۱۸ 18
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
جانهای خود را به صبر دریابید. ۱۹ 19
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
«و چون بینید که اورشلیم به لشکرهامحاصره شده است آنگاه بدانید که خرابی آن رسیده است. ۲۰ 20
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
آنگاه هر‌که در یهودیه باشد، به کوهستان فرار کند و هر‌که در شهر باشد، بیرون رود و هر‌که در صحرا بود، داخل شهر نشود. ۲۱ 21
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
زیرا که همان است ایام انتقام، تا آنچه مکتوب است تمام شود. ۲۲ 22
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
لیکن وای بر آبستنان وشیردهندگان در آن ایام، زیرا تنگی سخت برروی زمین و غضب بر این قوم حادث خواهد شد. ۲۳ 23
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
و به دم شمشیر خواهند افتاد و در میان جمیع امت‌ها به اسیری خواهند رفت و اورشلیم پایمال امت‌ها خواهد شد تا زمانهای امت‌ها به انجام رسد. ۲۴ 24
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
و در آفتاب و ماه و ستارگان علامات خواهد بود و بر زمین تنگی و حیرت از برای امت‌ها روی خواهد نمود به‌سبب شوریدن دریا وامواجش. ۲۵ 25
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
و دلهای مردم ضعف خواهد کرد از خوف و انتظار آن وقایعی که برربع مسکون ظاهرمی شود، زیرا قوات آسمان متزلزل خواهد شد. ۲۶ 26
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
و آنگاه پسر انسان را خواهند دید که بر ابری سوار شده با قوت و جلال عظیم می‌آید. ۲۷ 27
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
«و چون ابتدای این چیزها بشود راست شده، سرهای خود را بلند کنید از آن جهت که خلاصی شما نزدیک است.» ۲۸ 28
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
و برای ایشان مثلی گفت که «درخت انجیر و سایر درختان راملاحظه نمایید، ۲۹ 29
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
که چون می‌بینید شکوفه می‌کند خود می‌دانید که تابستان نزدیک است. ۳۰ 30
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
و همچنین شما نیز چون بینید که این امور واقع می‌شود، بدانید که ملکوت خدا نزدیک شده است. ۳۱ 31
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
هرآینه به شما می‌گویم که تا جمیع این امور واقع نشود، این فرقه نخواهد گذشت. ۳۲ 32
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
آسمان و زمین زایل می‌شود لیکن سخنان من زایل نخواهد شد. ۳۳ 33
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
پس خود را حفظ کنید مبادا دلهای شما ازپرخوری و مستی و اندیشه های دنیوی، سنگین گردد و آن روز ناگهان بر شما آید. ۳۴ 34
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
زیرا که مثل دامی بر جمیع سکنه تمام روی زمین خواهد آمد. ۳۵ 35
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
پس در هر وقت دعا کرده، بیدار باشید تاشایسته آن شوید که از جمیع این چیزهایی که به وقوع خواهد پیوست نجات یابید و در حضورپسر انسان بایستید.» ۳۶ 36
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
و روزها را در هیکل تعلیم می‌داد و شبها بیرون رفته، در کوه معروف به زیتون به‌سر می‌برد. ۳۷ 37
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
و هر بامداد قوم نزد وی در هیکل می‌شتافتند تا کلام او را بشنوند. ۳۸ 38
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< لوقا 21 >