< ایّوب 32 >

پس آن سه مرد از جواب دادن به ایوب باز ماندند چونکه او در نظر خود عادل بود. ۱ 1
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
آنگاه خشم الیهو ابن برکئیل بوزی که ازقبیله رام بود مشتعل شد، و غضبش بر ایوب افروخته گردید، از این جهت که خویشتن را ازخدا عادلتر می‌نمود. ۲ 2
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
و خشمش بر سه رفیق خود افروخته گردید، از این جهت که هر‌چندجواب نمی یافتند، اما ایوب را مجرم می‌شمردند. ۳ 3
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
و الیهو از سخن‌گفتن با ایوب درنگ نموده بود زیرا که ایشان در عمر، از وی بزرگتربودند. ۴ 4
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
اما چون الیهو دید که به زبان آن سه مردجوابی نیست، پس خشمش افروخته شد. ۵ 5
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
و الیهو ابن برکئیل بوزی به سخن آمده، گفت: «من در عمر صغیر هستم، و شما موسفید. بنابراین ترسیده، جرات نکردم که رای خود را برای شمابیان کنم. ۶ 6
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
و گفتم روزها سخن گوید، و کثرت سالها، حکمت را اعلام نماید. ۷ 7
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
لیکن در انسان روحی هست، و نفخه قادرمطلق، ایشان را فطانت می‌بخشد. ۸ 8
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
بزرگان نیستند که حکمت دارند، و نه پیران که انصاف را می‌فهمند. ۹ 9
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
بنابراین می‌گویم که مرا بشنو. و من نیز رای خود را بیان خواهم نمود. ۱۰ 10
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
اینک از سخن‌گفتن با شما درنگ نمودم، و براهین شما را گوش گرفتم. تا سخنان را کاوش گردید. ۱۱ 11
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
و من در شما تامل نمودم و اینک کسی از شما نبود که ایوب را ملزم سازد. یا سخنان او را جواب دهد. ۱۲ 12
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
مبادا بگویید که حکمت رادریافت نموده‌ایم، خدا او را مغلوب می‌سازد و نه انسان. ۱۳ 13
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
زیرا که سخنان خود را به ضد من ترتیب نداده است، و به سخنان شما او را جواب نخواهم داد. ۱۴ 14
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
ایشان حیران شده، دیگر جواب ندادند، وسخن از ایشان منقطع شد. ۱۵ 15
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
پس آیا من انتظاربکشم چونکه سخن نمی گویند؟ و ساکت شده، دیگر جواب نمی دهند؟ ۱۶ 16
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
پس من نیز از حصه خود جواب خواهم داد، و من نیز رای خود رابیان خواهم نمود. ۱۷ 17
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
زیرا که از سخنان، مملوهستم. و روح باطن من، مرا به تنگ می‌آورد. ۱۸ 18
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
اینک دل من مثل شرابی است که مفتوح نشده باشد، و مثل مشکهای تازه نزدیک است بترکد. ۱۹ 19
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
سخن خواهم راند تا راحت یابم و لبهای خودرا گشوده، جواب خواهم داد. ۲۰ 20
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
حاشا از من که طرفداری نمایم و به احدی کلام تملق‌آمیز گویم. ۲۱ 21
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
چونکه به گفتن سخنان تملق‌آمیز عارف نیستم. والا خالقم مرا به زودی خواهد برداشت. ۲۲ 22
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< ایّوب 32 >