< اشعیا 9 >

لیکن برای او که در تنگی می‌بود، تاریکی نخواهد شد. در زمان پیشین زمین زبولون وزمین نفتالی را ذلیل ساخت، اما در زمان آخر آن را به راه دریا به آن طرف اردن در جلیل امت هامحترم خواهد گردانید. ۱ 1
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
قومی که در تاریکی سالک می‌بودند، نور عظیمی خواهند دید و بر ساکنان زمین سایه موت نور ساطع خواهد شد. ۲ 2
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
تو قوم را بسیار ساخته، شادی ایشان را زیادگردانیدی. به حضور تو شادی خواهند کرد مثل شادمانی وقت درو و مانند کسانی که در تقسیم نمودن غنیمت وجد می‌نمایند. ۳ 3
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
زیرا که یوغ باراو را و عصای گردنش یعنی عصای جفا کننده وی را شکستی چنانکه در روز مدیان کردی. ۴ 4
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
زیرا همه اسلحه مسلحان در غوغا است ورخوت ایشان به خون آغشته است اما برای سوختن و هیزم آتش خواهند بود. ۵ 5
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
زیرا که برای ما ولدی زاییده و پسری به ما بخشیده شد وسلطنت بر دوش او خواهد بود و اسم او عجیب ومشیر و خدای قدیر و پدر سرمدی و سرورسلامتی خوانده خواهد شد. ۶ 6
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
ترقی سلطنت وسلامتی او را بر کرسی داود و بر مملکت وی انتهانخواهد بود تا آن را به انصاف و عدالت از الان تاابدالاباد ثابت و استوار نماید. غیرت یهوه صبایوت این را بجا خواهد آورد. ۷ 7
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
خداوند کلامی نزد یعقوب فرستاد و آن براسرائیل واقع گردید. ۸ 8
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
و تمامی قوم خواهنددانست یعنی افرایم و ساکنان سامره که از غرور وتکبر دل خود می‌گویند. ۹ 9
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
خشتها افتاده است امابا سنگهای تراشیده بنا خواهیم نمود؛ چوبهای افراغ در هم شکست اما سرو آزاد بجای آنهامی گذاریم. ۱۰ 10
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
بنابراین خداوند دشمنان رصین رابضد او خواهد برافراشت و خصمان او را خواهدبرانگیخت. ۱۱ 11
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
ارامیان را از مشرق و فلسطینیان رااز مغرب و ایشان اسرائیل را با دهان گشوده خواهند خورد. اما با این همه خشم او برگردانیده نشده و دست او هنوز دراز است. ۱۲ 12
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
و این قوم بسوی زننده خودشان بازگشت ننموده و یهوه صبایوت را نطلبیده‌اند. ۱۳ 13
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
بنابراین خداوند سر ودم و نخل و نی را از اسرائیل در یک روز خواهدبرید. ۱۴ 14
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
مرد پیر و مرد شریف سر است و نبی‌ای که تعلیم دروغ می‌دهد، دم می‌باشد. ۱۵ 15
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
زیرا که هادیان این قوم ایشان را گمراه می‌کنند و پیروان ایشان بلعیده می‌شوند. ۱۶ 16
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
از این سبب خداوند از جوانان ایشان مسرور نخواهد شد و بر یتیمان و بیوه‌زنان ایشان ترحم نخواهد نمود. چونکه جمیع ایشان منافق وشریرند و هر دهانی به حماقت متکلم می‌شود بااینهمه غضب او برگردانیده نشده و دست او هنوزدراز است. ۱۷ 17
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
زیرا که شرارت مثل آتش می‌سوزاند و خار و خس را می‌خورد، و دربوته های جنگل افروخته شده، دود غلیظ پیچان می‌شود. ۱۸ 18
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
از غضب یهوه صبایوت زمین سوخته شده است و قوم هیزم آتش گشته‌اند و کسی بربرادر خود شفقت ندارد. ۱۹ 19
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
از جانب راست می‌ربایند و گرسنه می‌مانند و از طرف چپ می‌خورند و سیر نمی شوند و هرکس گوشت بازوی خود را می‌خورد. ۲۰ 20
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
منسی افرایم را وافرایم منسی را و هر دوی ایشان بضد یهودا متحدمی شوند. با اینهمه غضب او برگردانیده نشده ودست او هنوز دراز است. ۲۱ 21
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.

< اشعیا 9 >