< اشعیا 52 >

بیدار شو‌ای صهیون! بیدار شو و قوت خود را بپوش‌ای شهر مقدس اورشلیم! لباس زیبایی خویش را در بر کن زیرا که نامختون و ناپاک بار دیگر داخل تو نخواهد شد. ۱ 1
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
‌ای اورشلیم خود را از گرد بیفشان و برخاسته، بنشین! و‌ای دختر صهیون که اسیر شده‌ای بندهای گردن خود را بگشا! ۲ 2
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
زیرا خداوند چنین می‌گوید: مفت فروخته کشتید و بی‌نقره فدیه داده خواهیدشد. ۳ 3
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
چونکه خداوند یهوه چنین می‌گوید: که درایام سابق قوم من به مصر فرود شدند تا در آنجاساکن شوند و بعد از آن آشور بر ایشان بی‌سبب ظلم نمودند. ۴ 4
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
اما الان خداوند می‌گوید: در اینجامرا چه‌کار است که قوم من مجان گرفتار شده‌اند. و خداوند می‌گوید: آنانی که بر ایشان تسلط دارندصیحه می‌زنند و نام من دائم هر روز اهانت می‌شود. ۵ 5
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
بنابراین قوم من اسم مرا خواهندشناخت. و در آن روز خواهند فهمید که تکلم کننده من هستم، هان من هستم. ۶ 6
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
چه زیبا است بر کوهها پایهای مبشر که سلامتی را ندا می‌کند و به خیرات بشارت می‌دهدو نجات را ندا می‌کند و به صهیون می‌گوید که خدای تو سلطنت می‌نماید. ۷ 7
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
آواز دیده بانان تواست که آواز خود را بلند کرده، با هم ترنم می‌نمایند زیرا وقتی که خداوند به صهیون رجعت می‌کند ایشان معاینه خواهند دید. ۸ 8
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
‌ای خرابه های اورشلیم به آواز بلند با هم ترنم نمایید، زیرا خداوند قوم خود را تسلی داده، و اورشلیم را فدیه نموده است. ۹ 9
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
خداوند ساعد قدوس خود را در نظر تمامی امت‌ها بالا زده است وجمیع کرانه های زمین نجات خدای ما را دیده‌اند. ۱۰ 10
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
‌ای شما که ظروف خداوند را برمی داریدبیکسو شوید بیکسو شوید و از اینجا بیرون رویدو چیز ناپاک را لمس منمایید و از میان آن بیرون رفته، خویشتن را طاهر سازید. ۱۱ 11
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
زیرا که به تعجیل بیرون نخواهید رفت و گریزان روانه نخواهید شد، چونکه یهوه پیش روی شماخواهد خرامید و خدای اسرائیل ساقه شماخواهد بود. ۱۲ 12
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
اینک بنده من با عقل رفتار خواهد کرد وعالی و رفیع و بسیار بلند خواهد شد. ۱۳ 13
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
چنانکه بسیاری از تو در عجب بودند (از آن جهت که منظر او از مردمان و صورت او از بنی آدم بیشترتباه گردیده بود). ۱۴ 14
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
همچنان بر امت های بسیارخواهد پاشید و به‌سبب او پادشاهان دهان خود را خواهند بست زیرا چیزهایی را که برای ایشان بیان نشده بود خواهند دید و آنچه را که نشنیده بودند خواهند فهمید. ۱۵ 15
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< اشعیا 52 >