< اشعیا 18 >

وای بر زمینی که در آن آواز بالها است که به آن طرف نهرهای کوش می‌باشد. ۱ 1
Kaiton ƙasar da ake jin ƙarar fikafikai a bakin kogunan Kush,
و ایلچیان به دریا و در کشتیهای بردی بر روی آبها می‌فرستد و می‌گوید: ای رسولان تیزروبروید نزد امت بلند قد و براق، نزد قومی که ازابتدایش تا کنون مهیب بوده‌اند یعنی امت زورآورو پایمال کننده که نهرها زمین ایشان را تقسیم می‌کند. ۲ 2
wadda ta aiko da jakadu ta teku cikin jiragen ruwan da aka yi da kyauro a bisa ruwa. Ku tafi, ku’yan saƙo masu sauri, zuwa ga dogayen mutane masu sulɓin jiki, zuwa ga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko tana jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba.
‌ای تمامی ساکنان ربع مسکون و سکنه جهان، چون علمی بر کوهها بلند گردد بنگرید وچون کرنا نواخته شود بشنوید. ۳ 3
Ku dukan mutanen duniya, ku da kuke zama a duniya, sa’ad da aka ɗaga tutar a kan duwatsu, za ku gan shi, sa’ad da kuma aka busa ƙaho, za ku ji shi.
زیرا خداوند به من چنین گفته است که من خواهم آرامید و ازمکان خود نظر خواهم نمود. مثل گرمای صاف برنباتات و مثل ابر شبنم دار در حرارت حصاد. ۴ 4
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Zan yi shiru in kuma duba a hankali daga mazaunina, kamar ƙuna mai zafi a hasken rana, kamar girgijen raba a lokacin girbi.”
زیرا قبل از حصاد وقتی که شکوفه تمام شود وگل به انگور رسیده، مبدل گردد او شاخه‌ها را بااره‌ها خواهد برید و نهالها را بریده دور خواهدافکند. ۵ 5
Gama kafin girbi, sa’ad da furanni suka karkaɗe furanni kuma suka zama’ya’yan inabin da suka nuna, zai faffalle rassan kuringar inabi da wuƙa, ya yanke ya kuma kwashe rassan da suka bazu.
و همه برای مرغان شکاری کوهها ووحوش زمین واگذاشته خواهد شد. و مرغان شکاری تابستان را بر آنها بسر خواهند برد وجمیع وحوش زمین زمستان را بر آنها خواهندگذرانید. ۶ 6
Duk za a bar su wa tsuntsayen dutse su ci da kuma namun jeji; tsuntsaye kuma za su ci rani a kansu, namun jeji kuma za su yi damina a kansu.
و در آن زمان هدیه‌ای برای یهوه صبایوت از قوم بلند قد و براق و از قومی که ازابتدایش تا کنون مهیب است و از امتی زورآور وپایمال کننده که نهرها زمین ایشان را تقسیم می‌کند به مکان اسم یهوه صبایوت یعنی به کوه صهیون آورده خواهد شد. ۷ 7
A wannan lokaci za a kawo kyautai wa Ubangiji Maɗaukaki daga dogayen mutane masu sulɓin jiki, daga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko na jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba. Za a kawo kyautai zuwa Dutsen Sihiyona, wurin da Sunan Ubangiji Maɗaukaki yake.

< اشعیا 18 >