< اشعیا 10 >

وای بر آنانی که احکام غیر عادله راجاری می‌سازند و کاتبانی که ظلم رامرقوم می‌دارند، ۱ 1
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
تا مسکینان را از داوری منحرف سازند و حق فقیران قوم مرا بربایند تا آنکه بیوه‌زنان غارت ایشان بشوند و یتیمان راتاراج نمایند. ۲ 2
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
پس در روز بازخواست در حینی که خرابی از دور می‌آید، چه خواهید کرد وبسوی که برای معاونت خواهید گریخت و جلال خود را کجا خواهید انداخت؟ ۳ 3
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
غیر از آنکه زیراسیران خم شوند و زیر کشتگان بیفتند. با اینهمه غضب او برگردانیده نشده و دست او هنوز درازاست. ۴ 4
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
وای بر آشور که عصای غضب من است. وعصایی که در دست ایشان است خشم من می‌باشد. ۵ 5
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
او را بر امت منافق می‌فرستم و نزد قوم مغضوب خود مامور می‌دارم، تا غنیمتی بربایندو غارتی ببرند و ایشان را مثل گل کوچه‌ها پایمال سازند. ۶ 6
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
اما او چنین گمان نمی کند و دلش بدینگونه قیاس نمی نماید، بلکه مراد دلش این است که امت های بسیار را هلاک و منقطع بسازد. ۷ 7
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
زیرا می‌گوید آیا سرداران من جمیع پادشاه نیستند؟ ۸ 8
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
آیا کلنو مثل کرکمیش نیست و آیاحمات مثل ارفاد نی، و آیا سامره مانند دمشق نمی باشد؟ ۹ 9
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
چنانکه دست من بر ممالک بتهااستیلا یافت و بتهای تراشیده آنها از بتهای اورشلیم و سامره بیشتر بودند. ۱۰ 10
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
پس آیا به نهجی که به سامره و بتهایش عمل نمودم به اورشلیم و بتهایش چنین عمل نخواهم نمود؟ ۱۱ 11
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
و واقع خواهد شد بعد از آنکه خداوندتمامی کار خود را با کوه صهیون و اورشلیم به انجام رسانیده باشد که من از ثمره دل مغرورپادشاه آشور و از فخر چشمان متکبر وی انتقام خواهم کشید. ۱۲ 12
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
زیرا می‌گوید: «به قوت دست خود و به حکمت خویش چونکه فهیم هستم این را کردم و حدود قومها را منتقل ساختم و خزاین ایشان را غارت نمودم و مثل جبار سروران ایشان را به زیر انداختم. ۱۳ 13
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
و دست من دولت قوم‌ها رامثل آشیانه‌ای گرفته است و به طوری که تخمهای متروک را جمع کنند من تمامی زمین راجمع کردم. و کسی نبود که بال را بجنباند یا دهان خود را بگشاید یا جک جک بنماید.» ۱۴ 14
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
آیا تبر بر کسی‌که به آن می‌شکند فخرخواهد نمود یا اره بر کسی‌که آن را می‌کشدافتخار خواهد کرد، که گویا عصا بلند کننده خودرا بجنباند یا چوب دست آنچه را که چوب نباشدبلند نماید؟ ۱۵ 15
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
بنابراین خداوند یهوه صبایوت برفربهان او لاغری خواهد فرستاد و زیر جلال اوسوختنی مثل سوختن آتش افروخته خواهد شد. ۱۶ 16
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
و نور اسرائیل نار و قدوس وی شعله خواهدشد، و در یکروز خار و خسش را سوزانیده، خواهد خورد. ۱۷ 17
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
و شوکت جنگل و بستان او هم روح و هم بدن را تباه خواهد ساخت و مثل گداختن مریض خواهد شد. ۱۸ 18
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
و بقیه درختان وجنگلش قلیل العدد خواهد بود که طفلی آنها راثبت تواند کرد. ۱۹ 19
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
و در آن روز واقع خواهد شد که بقیه اسرائیل و ناجیان خاندان یعقوب بار دیگر برزننده خودشان اعتماد نخواهند نمود. بلکه برخداوند که قدوس اسرائیل است به اخلاص اعتماد خواهند نمود. ۲۰ 20
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
و بقیه‌ای یعنی بقیه یعقوب بسوی خدای قادر مطلق بازگشت خواهند کرد. ۲۱ 21
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
زیرا هرچند قوم تو اسرائیل مثل ریگ دریا باشند فقط از ایشان بقیتی بازگشت خواهند نمود. هلاکتی که مقدر است به عدالت مجرا خواهد شد ۲۲ 22
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
زیرا خداوند یهوه صبایوت هلاکت و تقدیری در میان تمام زمین به عمل خواهد آورد. ۲۳ 23
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
بنابراین خداوند یهوه صبایوت چنین می‌گوید: «ای قوم من که در صهیون ساکنیداز آشور مترسید، اگر‌چه شما را به چوب بزند وعصای خود را مثل مصریان بر شما بلند نماید. ۲۴ 24
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
زیرا بعد از زمان بسیار کمی غضب تمام خواهد شد و خشم من برای هلاکت ایشان خواهد بود.» ۲۵ 25
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
و یهوه صبایوت تازیانه‌ای بر وی خواهد برانگیخت چنانکه در کشتار مدیان برصخره غراب. و عصای او بر دریا خواهد بود وآن را بلند خواهد کرد به طوری که بر مصریان کرده بود. ۲۶ 26
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
و در آن روز واقع خواهد شد که باراو از دوش تو و یوغ او از گردن تو رفع خواهد شدو یوغ از فربهی گسسته خواهد شد. ۲۷ 27
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
او به عیات رسید و از مجرون گذشت و درمکماش اسباب خود را گذاشت. ۲۸ 28
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
از معبر عبورکردند و در جبع منزل گزیدند، اهل رامه هراسان شدند و اهل جبعه شاول فرار کردند. ۲۹ 29
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
‌ای دخترجلیم به آواز خود فریاد برآور! ای لیشه و‌ای عناتوت فقیر گوش ده! ۳۰ 30
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
مدمینه فراری شدند وساکنان جیبیم گریختند. ۳۱ 31
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
همین امروز در نوب توقف می‌کند و دست خود را بر جبل دخترصهیون و کوه اورشلیم دراز می‌سازد. ۳۲ 32
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
اینک خداوند یهوه صبایوت شاخه‌ها را با خوف قطع خواهد نمود و بلند قدان بریده خواهند شد و مرتفعان پست خواهند گردید، ۳۳ 33
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
و بوته های جنگل به آهن بریده خواهد شد و لبنان به‌دست جباران خواهد افتاد. ۳۴ 34
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< اشعیا 10 >