< دوم سموئیل 24 >

و خشم خداوند بار دیگر بر اسرائیل افروخته شد. پس داود را بر ایشان برانگیزانیده، گفت: «برو و اسرائیل و یهودا رابشمار.» ۱ 1
Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
و پادشاه به‌سردار لشکر خود یوآب که همراهش بود، گفت: «الان در تمامی اسباطاسرائیل از دان تا بئرشبع گردش کرده، قوم رابشمار تا عدد قوم را بدانم.» ۲ 2
Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
و یوآب به پادشاه گفت: «حال یهوه، خدای تو، عدد قوم را هر‌چه باشد، صد چندان زیاده کند، و چشمان آقایم، پادشاه، این را ببیند، لیکن چرا آقایم، پادشاه، خواهش این عمل دارد؟» ۳ 3
Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
اما کلام پادشاه بریوآب و سرداران لشکر غالب آمد و یوآب وسرداران لشکر از حضور پادشاه برای شمردن قوم اسرائیل بیرون رفتند. ۴ 4
Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
و از اردن عبور کرده، در عروعیر به طرف راست شهری که در وسط وادی جاد در مقابل یعزیر است، اردو زدند. ۵ 5
Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
و به جلعاد و زمین تحتیم حدشی آمدند و به دان یعن رسیده، به سوی صیدون دور زدند. ۶ 6
Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
و به قلعه صور و تمامی شهرهای حویان و کنعانیان آمدند و به جنوب یهودا تا بئرشبع گذشتند. ۷ 7
Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
وچون در تمامی زمین گشته بودند، بعد ازانقضای نه ماه و بیست روز به اورشلیم مراجعت کردند. ۸ 8
Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
و یوآب عدد شمرده شدگان قوم را به پادشاه داد: از اسرائیل هشتصد هزار مردجنگی شمشیرزن و از یهودا پانصد هزار مردبودند. ۹ 9
Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
و داود بعد از آنکه قوم را شمرده بود، دردل خود پشیمان گشت. پس داود به خداوندگفت: «در این کاری که کردم، گناه عظیمی ورزیدم و حال‌ای خداوند گناه بنده خود را عفوفرما زیرا که بسیار احمقانه رفتار نمودم.» ۱۰ 10
Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
وبامدادان چون داود برخاست، کلام خداوند به‌جاد نبی که رایی داود بود، نازل شده، گفت: ۱۱ 11
Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
«برو داود را بگو خداوند چنین می‌گوید: سه چیز پیش تو می‌گذارم پس یکی از آنها را برای خود اختیار کن تا برایت به عمل آورم.» ۱۲ 12
“Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
پس جاد نزد داود آمده، او را مخبر ساخت و گفت: «آیا هفت سال قحط در زمینت برتو عارض شود، یا سه ماه از حضور دشمنان خود فرار نمایی وایشان تو را تعاقب کنند، یا وبا سه روز در زمین توواقع شود. پس الان تشخیص نموده، ببین که نزدفرستنده خود چه جواب ببرم.» ۱۳ 13
Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
داود به‌جادگفت: «در شدت تنگی هستم. تمنا اینکه به‌دست خداوند بیفتیم زیرا که رحمتهای او عظیم است وبه‌دست انسان نیفتم.» ۱۴ 14
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
پس خداوند وبا براسرائیل از آن صبح تاوقت معین فرستاد و هفتاد هزار نفر از قوم، از دان تا بئرشبع مردند. ۱۵ 15
Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
و چون فرشته، دست خود رابر اورشلیم دراز کرد تا آن را هلاک سازد، خداونداز آن بلا پشیمان شد و به فرشته‌ای که قوم راهلاک می‌ساخت گفت: «کافی است! حال دست خود را باز دار.» و فرشته خداوند نزد خرمنگاه ارونه یبوسی بود. ۱۶ 16
Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
و چون داود، فرشته‌ای را که قوم را هلاک می‌ساخت دید، به خداوند عرض کرده، گفت: «اینک من گناه کرده‌ام و من عصیان ورزیده‌ام اما این گوسفندان چه کرده‌اند؟ تمنااینکه دست تو بر من و برخاندان پدرم باشد.» ۱۷ 17
Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
و در آن روز جاد نزد داود آمده، گفت: «بروو مذبحی در خرمنگاه ارونه یبوسی برای خداوندبرپا کن.» ۱۸ 18
A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
پس داود موافق کلام جاد چنانکه خداوند امر فرموده بود، رفت. ۱۹ 19
Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
و چون ارونه نظر انداخته، پادشاه و بندگانش را دید که نزد وی می‌آیند، ارونه بیرون آمده، به حضور پادشاه به روی خود به زمین افتاده، تعظیم نمود. ۲۰ 20
Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
و ارونه گفت: «آقایم، پادشاه، چرا نزد بنده خود آمده است؟» داود گفت: «تا خرمنگاه را از تو بخرم ومذبحی برای خداوند بنا نمایم و تا وبا از قوم رفع شود.» ۲۱ 21
Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
و ارونه به داود عرض کرد: «آقایم پادشاه آنچه را که در نظرش پسند آیدگرفته، قربانی کند و اینک گاوان به جهت قربانی سوختنی و چومها و اسباب گاوان به جهت هیزم. این همه را‌ای پادشاه، ارونه به پادشاه می‌دهد. و ارونه به پادشاه گفت: «یهوه، خدایت، تو را قبول فرماید.» ۲۲ 22
Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
اما پادشاه به ارونه گفت: «نی، بلکه البته به قیمت از توخواهم گرفت، و برای یهوه، خدای خود، قربانی های سوختنی بی‌قیمت نخواهم گذرانید.» پس داود خرمنگاه و گاوان را به پنجاه مثقال نقره خرید. ۲۳ 23
Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
و داود در آنجا مذبحی برای خداوند بنانموده، قربانی های سوختنی و ذبایح سلامتی گذرانید. پس خداوند به جهت زمین اجابت فرمود و وبا از اسرائیل رفع شد. گذرانید. پس خداوند به جهت زمین اجابت فرمود و وبا از اسرائیل رفع شد. ۲۴ 24
Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
۲۵ 25
Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.

< دوم سموئیل 24 >