< اول سموئیل 16 >

و خداوند به سموئیل گفت: «تا به کی توبرای شاول ماتم می‌گیری چونکه من اورا از سلطنت نمودن بر اسرائیل رد نمودم. پس حقه خود را از روغن پر کرده، بیا تا تو را نزد یسای بیت لحمی بفرستم، زیرا که از پسرانش پادشاهی برای خود تعیین نموده‌ام.» ۱ 1
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
سموئیل گفت: «چگونه بروم. اگر شاول بشنود مرا خواهدکشت.» خداوند گفت: «گوساله‌ای همراه خود ببرو بگو که به جهت گذرانیدن قربانی برای خداوندآمده‌ام. ۲ 2
Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
و یسا را به قربانی دعوت نما، و من تو رااعلام می‌نمایم که چه باید بکنی، و کسی را که به تو امر نمایم برای من مسح نما.» ۳ 3
Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
و سموئیل آنچه را که خداوند به او گفته بود بجا آورده، به بیت لحم آمد، و مشایخ شهر لرزان شده، به استقبال او آمدند، و گفتند: «آیا با سلامتی می‌آیی؟» ۴ 4
Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
گفت: «با سلامتی به جهت قربانی گذرانیدن برای خداوند آمده‌ام، پس خود را تقدیس نموده، همراه من به قربانی بیایید.» و اویسا و پسرانش را تقدیس نموده، ایشان را به قربانی دعوت نمود. ۵ 5
Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
و واقع شد که چون آمدند بر الیاب نظرانداخته، گفت: «یقین مسیح خداوند به حضوروی است.» ۶ 6
Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
اما خداوند به سموئیل گفت: «به چهره‌اش و بلندی قامتش نظر منما زیرا او را ردکرده‌ام، چونکه خداوند مثل انسان نمی نگرد، زیرا که انسان به ظاهر می‌نگرد و خداوند به دل می‌نگرد.» ۷ 7
Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
و یسا ابیناداب را خوانده، او را ازحضور سموئیل گذرانید، و او گفت: «خداوند این را نیز برنگزیده است.» ۸ 8
Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
و یسا شماه را گذرانید واو گفت: «خداوند این را نیز برنگزیده است.» ۹ 9
Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
ویسا هفت پسر خود را از حضور سموئیل گذرانیدو سموئیل به یسا گفت: «خداوند اینها رابرنگزیده است.» ۱۰ 10
Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
و سموئیل به یسا گفت: «آیا پسرانت تمام شدند.» گفت: «کوچکتر هنوز باقی است و اینک او گله را می‌چراند.» و سموئیل به یسا گفت: «بفرست و او را بیاور، زیرا که تا او به اینجا نیایدنخواهیم نشست.» ۱۱ 11
Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
پس فرستاده، او را آورد، واو سرخ رو و نیکوچشم و خوش منظر بود. وخداوند گفت: «برخاسته، او را مسح کن زیرا که همین است.» ۱۲ 12
Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
پس سموئیل حقه روغن راگرفته، او را در میان برادرانش مسح نمود، و از آن روز به بعد روح خداوند بر داود مستولی شد، وسموئیل برخاسته، به رامه رفت. ۱۳ 13
Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
و روح خداوند از شاول دور شد، و روح بداز جانب خداوند او را مضطرب می‌ساخت. ۱۴ 14
To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
وبندگان شاول وی را گفتند: «اینک روح بد از جانب خدا تو را مضطرب می‌سازد. ۱۵ 15
Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
پس آقای ما بندگان خود را که به حضورت هستند امرفرماید تا کسی را که بر بربط نواختن ماهر باشدبجویند، و چون روح بد از جانب خدا بر تو بیایدبه‌دست خود بنوازد، و تو را نیکو خواهد شد.» ۱۶ 16
Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
و شاول به بندگان خود گفت: «الان کسی را که به نواختن ماهر باشد برای من پیدا کرده، نزد من بیاورید.» ۱۷ 17
Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
و یکی از خادمانش در جواب وی گفت: «اینک پسر یسای بیت لحمی را دیدم که به نواختن ماهر و صاحب شجاعت و مرد جنگ آزموده و فصیح زبان و شخص نیکو صورت است و خداوند با وی می‌باشد.» ۱۸ 18
Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
پس شاول قاصدان نزد یسا فرستاده، گفت: «پسرت داود را که با گوسفندان است، نزد من بفرست.» ۱۹ 19
Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
آنگاه یسا یک بار الاغ از نان و یک مشگ شراب و یک بزغاله گرفته، به‌دست پسرخود داود نزد شاول فرستاد. ۲۰ 20
Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
و داود نزد شاول آمده، به حضور وی ایستاد و او وی را بسیاردوست داشت و سلاحدار او شد. ۲۱ 21
Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
و شاول نزدیسا فرستاده، گفت: «داود نزد من بماند زیرا که به نظرم پسند آمد.» ۲۲ 22
Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
و واقع می‌شد هنگامی که روح بد از جانب خدا بر شاول می‌آمد که داودبربط گرفته، به‌دست خود می‌نواخت، و شاول راراحت و صحت حاصل می‌شد و روح بد از اومی رفت. ۲۳ 23
Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.

< اول سموئیل 16 >