< اول قرنتیان 1 >

پولس به اراده خدا رسول خوانده شده عیسی مسیح و سوستانیس برادر، ۱ 1
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
به کلیسای خدا که در قرنتس است، ازمقدسین در مسیح عیسی که برای تقدس خوانده شده‌اند، با همه کسانی که در هرجا نام خداوند ماعیسی مسیح را می‌خوانند که (خداوند) ما و(خداوند) ایشان است. ۲ 2
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
فیض و سلامتی ازجانب پدر ما خدا و عیسی مسیح خداوند بر شماباد. ۳ 3
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
خدای خود را پیوسته شکر می‌کنم درباره شما برای آن فیض خدا که در مسیح عیسی به شما عطا شده است، ۴ 4
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
زیرا شما از هرچیز دروی دولتمند شده‌اید، در هر کلام و در هرمعرفت. ۵ 5
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
چنانکه شهادت مسیح در شما استوارگردید، ۶ 6
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
بحدی که در هیچ بخشش ناقص نیستیدو منتظر مکاشفه خداوند ما عیسی مسیح می‌باشید. ۷ 7
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
که او نیز شما را تا آخر استوار خواهدفرمود تا در روز خداوند ما عیسی مسیح بی‌ملامت باشید. ۸ 8
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
امین است خدایی که شما را به شراکت پسر خود عیسی مسیح خداوند ماخوانده است. ۹ 9
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
لکن‌ای برادران از شما استدعا دارم به نام خداوند ما عیسی مسیح که همه یک سخن گوییدو شقاق در میان شما نباشد، بلکه در یک فکر ویک رای کامل شوید. ۱۰ 10
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
زیرا که‌ای برادران من، از اهل خانه خلوئی درباره شما خبر به من رسیدکه نزاعها در میان شما پیدا شده است. ۱۱ 11
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
غرض اینکه هریکی از شما می‌گوید که من از پولس هستم، و من از اپلس، و من از کیفا، و من از مسیح. ۱۲ 12
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
آیا مسیح منقسم شد؟ یا پولس در راه شمامصلوب گردید؟ یا به نام پولس تعمید یافتید؟ ۱۳ 13
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
خدا را شکر می‌کنم که هیچ‌یکی از شما راتعمید ندادم جز کرسپس و قایوس، ۱۴ 14
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
که مباداکسی گوید که به نام خود تعمید دادم. ۱۵ 15
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
وخاندان استیفان را نیز تعمید دادم و دیگر یادندارم که کسی را تعمید داده باشم. ۱۶ 16
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
زیرا که مسیح مرا فرستاد، نه تا تعمید دهم بلکه تا بشارت رسانم، نه به حکمت کلام مبادا صلیب مسیح باطل شود. ۱۷ 17
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
زیرا ذکر صلیب برای هالکان حماقت است، لکن نزد ما که ناجیان هستیم قوت خداست. ۱۸ 18
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
زیرا مکتوب است: «حکمت حکما را باطل سازم و فهم فهیمان را نابود گردانم.» ۱۹ 19
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
کجا است حکیم؟ کجا کاتب؟ کجا مباحث این دنیا؟ مگرخدا حکمت جهان را جهالت نگردانیده است؟ (aiōn g165) ۲۰ 20
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn g165)
زیرا که چون برحسب حکمت خدا، جهان ازحکمت خود به معرفت خدا نرسید، خدا بدین رضا داد که بوسیله جهالت موعظه، ایمانداران رانجات‌بخشد. ۲۱ 21
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
چونکه یهود آیتی می‌خواهند ویونانیان طالب حکمت هستند. ۲۲ 22
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
لکن ما به مسیح مصلوب وعظ می‌کنیم که یهود را لغزش و امت هارا جهالت است. ۲۳ 23
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
لکن دعوت‌شدگان را خواه یهود و خواه یونانی مسیح قوت خدا و حکمت خدا است. ۲۴ 24
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
زیرا که جهالت خدا از انسان حکیمتر است و ناتوانی خدا از مردم، تواناتر. ۲۵ 25
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
زیرا‌ای برادران دعوت خود را ملاحظه نمایید که بسیاری بحسب جسم حکیم نیستند وبسیاری توانا نی و بسیاری شریف نی. ۲۶ 26
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
بلکه خدا جهال جهان را برگزید تا حکما را رسوا سازدو خدا ناتوانان عالم را برگزید تا توانایان را رسواسازد، ۲۷ 27
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
و خسیسان دنیا و محقران را خدابرگزید، بلکه نیستیها را تا هستیها را باطل گرداند. ۲۸ 28
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
تا هیچ بشری در حضور او فخر نکند. ۲۹ 29
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
لکن از او شما هستید در عیسی مسیح که از جانب خدابرای شما حکمت شده است و عدالت قدوسیت و فدا. ۳۰ 30
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
تا چنانکه مکتوب است هر‌که فخر کنددر خداوند فخر نماید. ۳۱ 31
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”

< اول قرنتیان 1 >