< Romerne 4 >

1 Kva skal me då segja at Abraham, far vår, hev vunne etter kjøtet?
Me kenan zamu ce game da Ibrahim, kakanmu a jiki, me ya samu?
2 For vart Abraham rettferdiggjord av gjerningar, so hev han noko å rosa seg av. Men det hev han ikkje for Gud.
Domin idan Ibrahim ya sami kubutarwa ta wurin ayuka, ai da ya sami dalilin fahariya, amma ba a gaban Allah ba.
3 For kva segjer Skrifti? «Abraham trudde Gud, og det vart rekna honom til rettferd.»
Kuma fa me nassi ke fadi? “Ibrahim ya bada gaskiya ga Allah, sai aka lisafta ta adalci gare shi.”
4 Men den som held seg til gjerningar, honom vert løni ikkje tilrekna av nåde, men etter skyldnad;
Yanzu fa shi dake yin ayyuka, ladansa ba a lisafta shi alheri ba ne, amma abun da ke nasa.
5 men den som ikkje held seg til gjerningar, men trur på han som gjer den ugudlege rettferdig, honom vert trui hans rekna til rettferd.
Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.
6 Soleis prisar og David det menneskjet sælt som Gud tilreknar rettferd utan gjerningar:
Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka.
7 «Sæle er dei som hev misgjerderne sine forlatne og synderne sine yverbreidde.
Sai ya ce, “Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke.
8 Sæl er den mann som Herren ikkje tilreknar synd.»
Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba.”
9 Gjeld no denne sælkingi dei umskorne, eller dei u-umskorne og? For me segjer at trui vart rekna Abraham til rettferd.
To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, “Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi.”
10 Korleis vart ho då tilrekna honom? då han var umskoren, eller då han hadde fyrehud? Ikkje då han var umskoren, men då han hadde fyrehud,
Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.
11 og han fekk umskjeringsteiknet til innsigle på rettferdi ved den trui som han hadde då han var u-umskoren, av di han skulde vera far til alle dei u-umskorne som trur, so rettferdi kunde verta tilrekna deim og,
Ibrahim ya amshi alamar kaciya. Wannan shi ne hatimin adalcin bangaskiyar da ya ke da ita tun cikin rashin kaciyarsa. Albarkacin wannan alama ce, ta sa shi ya zama uban dukkan wadanda suka badagaskiya, ko da shike ba su da kaciya. Wato ma'ana, adalci za a lisafta masu.
12 og far til dei umskorne, dei som ikkje berre hev umskjering, men og gjeng i fotfaret av den trui som Abraham, far vår, hadde då han var u-umskoren.
Wannan kuma yana da ma'anar cewa Ibrahim ya zama uban kaciya ga wadanda suka fito ba domin masu kaciya kadai ba, amma kuma domin wadanda ke biyo matakin ubanmu Ibrahim. Kuma wannan itace bangaskiyar da ya ke da ita a rashin kaciya.
13 For ikkje ved lovi fekk Abraham eller ætti hans den lovnaden at han skulde vera erving til verdi, men ved tru-rettferd.
Domin ba ta wurin shari'a aka bada alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa ba, wannan alkawarin da ya ce zasu gaji duniya. Maimako, a ta wurin adalcin bangaskiya ne.
14 For er dei som held seg til lovi ervingar, so hev trui vorte gagnlaus og lovnaden til inkjes;
Domin idan su da ke na shari'a magada ne, bangaskiya bata da komai, kuma alkawarin an wofintar da shi kenan.
15 for lovi verkar vreide, men der det ingi lov er, der er ikkje heller lovbrot.
Domin shari'a ta kan jawo fushi, amma ta wurin rashin shari'a, babu karya umarni.
16 Difor fekk han lovnaden ved trui, so det kunde vera som ein nåde, so lovnaden kunde standa fast for all ætti, ikkje berre for den som hev lovi, men og for den som hev Abrahams tru; han som er far til oss alle -
Saboda wannan dalili haka ta faru ta wurin bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri. Kamar haka, alkawarin ya tabbata ga dukkan zuriya. Kuma wannan zuriya ba zata kunshi wadanda suke da sanin shari'a ba kadai, har ma da wadanda ke daga bangaskiyar Ibrahim. Saboda shi ne uban dukkan kowa,
17 som skrive stend: «Til fader åt mange folk hev eg sett deg» - for Guds åsyn som han trudde på, han som gjer dei daude livande og kallar det som ikkje er til, som um det vore til.
kamar yadda aka rubuta, “Na maishe ka uba ga kasashe masu yawa.” Ibrahim na gaban aminin sa, wato, Allah, mai bada rai ga mattatu kuma ya kan kira abubuwan da basu da rai su kuma kasance.
18 Mot von trudde han med von, so han skulde verta far til mange folk, etter det som sagt var: «So skal ætti di verta.»
Duk da halin da ke a bayyane, Ibrahim ya gaskata ga Allah kai tsaye game da abubuwan da ke nan gaba. Sai ya zama uba ga kasashe masu yawa, kamar yadda aka ambata, “... Haka zuriyarka zata kasance.”
19 Og utan veikskap i trui såg han på sin eigen likam, som var utlivd, han var nære på hundrad år, og på det utdøydde morslivet hennar Sara;
Ba ya karaya a bangaskiya ba. Ibrahim ya yarda da cewa jikinsa ya rigaya ya tsufa (shekarun sa na misalin dari). Ya kuma yarda da cewa mahaifar Saratu bata iya bada 'ya'ya ba.
20 men på Guds lovnad tvila han ikkje med vantru, men vart sterk i trui, med di han gav Gud æra
Amma domin alkawarin Allah, Ibrahim bai ji nauyin rashin bangaskiya ba. Maimakon haka, ya sami karfafawa a bangaskiyarsa sai ya daukaka Allah.
21 og var fullviss på at det han hadde lova, var han og megtig til å gjera.
Ya na da cikakkiyar gamsuwa cewa idan Allah ya yi alkawari, shi mai iya kammalawa ne.
22 Difor vart det og rekna honom til rettferd.
Haka nan ne kuma aka lisafta masa wannan a matsayin adalci.
23 Men ikkje berre for hans skuld er det skrive at det vart honom tilrekna,
To ba'a rubuta kawai damin amfaninsa kadai ba, da aka lisafta dominsa.
24 men og for vår skuld som det skal verta tilrekna, me som trur på honom som vekte upp Jesus, vår Herre, frå dei daude,
A rubuce yake domin mu, domin wadanda za'a lisafta su, mu da muka bada gaskiya gare shi wanda ya tada Yesu Ubangijinmu daga matattu.
25 han som vart gjeven for våre brot og uppvekt til vår rettferdiggjering.
Wannan shi ne wanda aka bashe shi domin zunubanmu kuma an tada shi saboda fasar mu.

< Romerne 4 >