< Sefanias 1 >

1 Dette er Herrens ord som kom til Sefanias, sønn av Kusi, sønn av Gedalja, sønn av Amarja, sønn av Esekias, i de dager da Josias, Amons sønn, var konge i Juda.
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 Bort, bort vil jeg ta alt av jorden, sier Herren.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 Jeg vil ta bort mennesker og dyr, ta bort himmelens fugler og havets fisker og alt det som volder anstøt, sammen med de ugudelige, og jeg vil utrydde menneskene av jorden, sier Herren.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 Jeg vil rekke min hånd ut mot Juda og mot alle Jerusalems innbyggere, og jeg vil utrydde av dette sted alt som er igjen av Ba'al, avgudsprestenes navn sammen med prestene
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 og dem som på takene tilbeder himmelens hær, og dem som tilbeder Herren og sverger ham troskap, men på samme tid sverger ved sin konge,
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 og dem som har vendt sig bort fra Herren, og som ikke har søkt Herren og ikke spurt efter ham.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Vær stille for Herren, Israels Gud! For Herrens dag er nær; Herren har stelt til en offerslaktning, han har innvidd sine gjester.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 Og på Herrens offerslaktnings dag vil jeg hjemsøke høvdingene og kongens sønner og alle som klær sig i utenlandske klær.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 Og jeg vil på den dag hjemsøke hver den som hopper over dørtreskelen, dem som fyller sin Herres hus med vold og svik.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 På den dag, sier Herren, skal det lyde skrik fra Fiskeporten og hyl fra stadens andre del og stort brak fra haugene.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Hyl, I som bor i Morteren! For hele kana'anitterfolket er utslettet; alle de som slepte på masser av sølv, er utryddet.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 Og på den samme tid vil jeg ransake Jerusalem med lykter, og jeg vil hjemsøke de folk som ligger på sin berme og sier i sitt hjerte: Herren gjør hverken godt eller ondt.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 Og deres gods skal bli til rov, og deres hus ødelegges; de skal bygge hus, men ikke bo i dem, og plante vingårder, men ikke drikke vin fra dem.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 Nær er Herrens dag, den store; den er nær og kommer med stor hast. Hør! Det er Herrens dag! Full av angst skriker da kjempen.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 En vredes dag er den dag, en dag med nød og trengsel, en dag med omstyrtelse og ødeleggelse, en dag med mørke og mulm, en dag med skyer og skodde,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 en dag med basunklang og hærskrik mot de faste byer og de høie murtinder.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 Da vil jeg sette slik angst i menneskene at de går der som blinde, fordi de har syndet mot Herren; og deres blod skal utøses som støv, og deres kjøtt som møkk.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Hverken deres sølv eller deres gull skal kunne berge dem på Herrens vredes dag; ved hans nidkjærhets ild skal hele jorden bli fortært; for han vil gjøre ende, ja brått gjøre ende på alle dem som bor på jorden.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Sefanias 1 >