< Romerne 10 >

1 Brødre! mitt hjertes ønske og min bønn til Gud for dem er at de må bli frelst.
’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
2 For jeg gir dem det vidnesbyrd at de har nidkjærhet for Gud, men ikke med skjønnsomhet;
Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
3 for da de ikke kjente Guds rettferdighet og strevde efter å grunne sin egen rettferdighet, gav de sig ikke inn under Guds rettferdighet.
Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
4 For Kristus er lovens ende, til rettferdighet for hver den som tror.
Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
5 For Moses skriver om rettferdigheten av loven: Det menneske som gjør disse ting, skal leve ved dem;
Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
6 men rettferdigheten av troen sier så: Si ikke i ditt hjerte: Hvem skal fare op til himmelen - det vil si: for å hente Kristus ned -?
Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
7 eller: Hvem skal fare ned i avgrunnen - det vil si: for å hente Kristus op fra de døde -? (Abyssos g12)
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
8 Men hvad sier den? Ordet er dig nær, i din munn og i ditt hjerte; det er troens ord, det som vi forkynner,
Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
9 for dersom du med din munn bekjenner at Jesus er Herre, og i ditt hjerte tror at Gud opvakte ham fra de døde, da skal du bli frelst;
Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 for med hjertet tror en til rettferdighet, og med munnen bekjenner en til frelse.
Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
11 For Skriften sier: Hver den som tror på ham, skal ikke bli til skamme.
Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
12 Det er jo ingen forskjell på jøde og greker; de har alle den samme Herre, som er rik nok for alle som påkaller ham;
Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
13 for hver den som påkaller Herrens navn, skal bli frelst.
gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
14 Hvorledes kan de da påkalle den som de ikke tror på? og hvorledes kan de tro der de ikke har hørt? og hvorledes kan de høre uten at det er nogen som forkynner?
To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
15 og hvorledes kan de forkynne uten at de blir utsendt? som skrevet er: Hvor fagre deres føtter er som forkynner fred, som bærer godt budskap!
Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
16 Men ikke alle var lydige mot evangeliet. For Esaias sier: Herre! hvem trodde vel det han hørte av oss?
Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
17 Så kommer da troen av forkynnelsen, og forkynnelsen ved Kristi ord;
Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
18 men jeg sier: Har de da ikke fått høre? Jo til visse; deres røst gikk ut til all jorden, og deres ord til jorderikes ende.
Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
19 Men jeg sier: Kjente da Israel ikke til det? Først sier Moses: Jeg vil gjøre eder nidkjære på det som ikke er et folk; på et uforstandig folk vil jeg gjøre eder harme;
Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
20 og Esaias våger sig til å si: Jeg blev funnet av dem som ikke søkte mig; jeg åpenbarte mig for dem som ikke spurte efter mig;
Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
21 men om Israel sier han: Hele dagen rakte jeg mine hender ut til et ulydig og gjenstridig folk.
Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”

< Romerne 10 >