< Salmenes 99 >

1 Herren er blitt konge, folkene bever, han som troner over kjeruber, jorden ryster.
Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
2 Herren er stor i Sion, og ophøiet er han over alle folkene.
Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
3 De skal prise ditt navn, det store og forferdelige; hellig er han.
Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
4 Og i sin styrke elsker kongen rettferd; du har grunnfestet rettvishet, du har gjort rett og rettferdighet i Jakob.
Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
5 Ophøi Herren vår Gud, og kast eder ned for hans føtters skammel! Hellig er han.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
6 Moses og Aron var blandt hans prester, og Samuel blandt dem som påkalte hans navn; de ropte til Herren, og han svarte dem.
Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
7 I en skystøtte talte han til dem; de holdt hans vidnesbyrd og den lov han gav dem.
Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
8 Herre vår Gud, du svarte dem; du var dem en Gud som tilgav dem, men også en hevner over deres gjerninger.
Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
9 Ophøi Herren vår Gud, og kast eder ned for hans hellige berg! For hellig er Herren vår Gud.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.

< Salmenes 99 >