< Salmenes 82 >

1 En salme av Asaf. Gud står i Guds menighet; midt iblandt guder holder han dom:
Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
2 Hvor lenge vil I dømme urettferdig og holde med de ugudelige? (Sela)
“Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
3 Døm den ringe og farløse, la den elendige og fattige få sin rett!
Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
4 Redd den ringe og trengende, frels ham fra de ugudeliges hånd!
Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
5 De skjønner intet, og de forstår intet, de vandrer i mørke; alle jordens grunnvoller vakler.
“Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
6 Jeg har sagt: I er guder, og I er alle den Høiestes sønner.
“Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
7 Men sannelig, som mennesker skal I dø, og som en av fyrstene skal I falle.
Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
8 Reis dig, Gud, hold dom over jorden! For du har alle hedningene i eie!
Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.

< Salmenes 82 >