< Salmenes 56 >

1 Til sangmesteren; efter "Den målløse due på de fjerne steder"; av David; en gyllen sang da filistrene grep ham i Gat. Vær mig nådig, Gud! for mennesker vil opsluke mig; hele dagen trenger de mig med krig.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Mine fiender søker å opsluke mig hele dagen; for mange er de som strider mot mig i overmot.
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 På den dag jeg frykter, setter jeg min lit til dig.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 Ved Gud priser jeg hans ord; til Gud setter jeg min lit, jeg frykter ikke; hvad skulde kjød kunne gjøre mig?
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 Hele dagen forvender de mine ord; alle deres tanker er mig imot til det onde.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 De slår sig sammen, de lurer, de tar vare på mine trin, fordi de står mig efter livet.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 Skulde de undslippe tross sin ondskap? Støt folkeslag ned i vrede, Gud!
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 Hvor ofte jeg har flyktet, det har du tellet; mine tårer er gjemt i din flaske; står de ikke i din bok?
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 Da skal mine fiender vende tilbake, på den dag jeg roper; dette vet jeg at Gud er med mig.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 Ved Gud priser jeg ordet; ved Herren priser jeg ordet.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 Til Gud setter jeg min lit, jeg frykter ikke; hvad skulde et menneske kunne gjøre mig?
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 På mig, Gud, hviler løfter til dig; jeg vil betale dig med takksigelser.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 For du har fridd min sjel fra døden, ja mine føtter fra fall, så jeg kan vandre for Guds åsyn i de levendes lys.
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.

< Salmenes 56 >