< Salmenes 27 >

1 Av David. Herren er mitt lys og min frelse, for hvem skal jeg frykte? Herren er mitt livs vern, for hvem skal jeg reddes?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 Når ugjerningsmenn nærmer sig imot mig for å opsluke mig, mine motstandere og mine fiender, så snubler og faller de selv.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Om en hær leirer sig imot mig, frykter ikke mitt hjerte; om krig reiser sig imot mig, enda er jeg trygg.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 Én ting har jeg bedt Herren om, det stunder jeg efter, at jeg må bo i Herrens hus alle mitt livs dager for å skue Herrens liflighet og grunde i hans tempel.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 For han gjemmer mig i sin hytte på den onde dag, han skjuler mig i sitt telts skjul; på en klippe fører han mig op.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 Og nu skal mitt hode opløfte sig over mine fiender rundt omkring mig, og jeg vil ofre jubeloffere i hans telt, jeg vil prise og lovsynge Herren.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Hør, Herre, høit roper jeg, og vær mig nådig og svar mig!
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 Mitt hjerte holder frem for dig ditt ord: Søk mitt åsyn! Herre, jeg søker ditt åsyn.
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Skjul ikke ditt åsyn for mig, bortstøt ikke i vrede din tjener! Min hjelp har du vært. Kast mig ikke bort og forlat mig ikke, min frelses Gud!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 For min far og min mor har forlatt mig, men Herren tar mig op.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Lær mig, Herre, din vei, og led mig på den jevne sti for mine fienders skyld!
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Overgi mig ikke til mine fienders mordlyst! for falske vidner står op imot mig, og menn som fnyser av vold.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 O, dersom jeg ikke trodde å skulle se Herrens godhet i de levendes land! -
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Bi på Herren, vær ved godt mot, og ditt hjerte være sterkt, ja, bi på Herren!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.

< Salmenes 27 >