< Salmenes 21 >

1 Til sangmesteren; en salme av David. Herre! Kongen gleder sig over din makt, og hvor høit han fryder sig ved din frelse!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Hvad hans hjerte ønsket, har du gitt ham, og hvad hans leber bad om, har du ikke nektet ham. (Sela)
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 For du kom ham i møte med velsignelse og lykke, du satte en krone av gull på hans hode.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Han bad dig om liv; du gav ham det, et langt liv evindelig og alltid.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Stor er hans ære ved din frelse; høihet og herlighet legger du på ham.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 For du setter ham til velsignelse evindelig, du fryder ham med glede for ditt åsyn.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 For kongen setter sin lit til Herren, og ved den Høiestes miskunnhet skal han ikke rokkes.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 Din hånd skal finne alle dine fiender, din høire hånd skal finne dine avindsmenn.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Du skal gjøre dem som en ildovn når du viser ditt åsyn; Herren skal opsluke dem i sin vrede, og ild skal fortære dem.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Deres frukt skal du utslette av jorden, og deres avkom blandt menneskenes barn.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 For de har grundet på ondt mot dig, de har uttenkt onde råd; de skal ikke makte noget.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 For du skal få dem til å vende ryggen; med dine buestrenger sikter du mot deres åsyn.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Reis dig, Herre, i din kraft! Vi vil lovsynge og prise ditt storverk.
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.

< Salmenes 21 >