< Salmenes 143 >

1 En salme av David. Herre, hør min bønn, vend øret til mine inderlige bønner, svar mig i din trofasthet, i din rettferdighet,
Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
2 og gå ikke i rette med din tjener! For ingen som lever, er rettferdig for ditt åsyn.
Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
3 For fienden har forfulgt min sjel, han har knust mitt liv til jorden, han har satt mig på mørke steder som de evig døde.
Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
4 Og min ånd er vansmektet i mig, mitt hjerte er forferdet inneni mig.
Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
5 Jeg kommer fordums dager i hu, jeg tenker på alt ditt verk, jeg grunder på dine henders gjerning.
Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
6 Jeg utbreder mine hender til dig, min sjel lenges efter dig som et vansmektende land. (Sela)
Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
7 Skynd dig å svare mig, Herre! Min ånd fortæres; skjul ikke ditt åsyn for mig, så jeg blir lik dem som farer ned i graven!
Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
8 La mig årle høre din miskunnhet, for til dig setter jeg min lit! Kunngjør mig den vei jeg skal vandre, for til dig opløfter jeg min sjel!
Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
9 Fri mig fra mine fiender, Herre! Hos dig søker jeg ly.
Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
10 Lær mig å gjøre din vilje, for du er min Gud! Din gode Ånd lede mig på jevnt land!
Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
11 For ditt navns skyld, Herre, vil du holde mig i live; i din rettferdighet vil du føre min sjel ut av trengsel,
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
12 og i din miskunnhet vil du utrydde mine fiender og ødelegge alle dem som trenger min sjel; for jeg er din tjener.
A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.

< Salmenes 143 >