< Salmenes 110 >

1 Av David; en salme. Herren sa til min herre: Sett dig ved min høire hånd, til jeg får lagt dine fiender til skammel for dine føtter!
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 Ditt veldes kongestav skal Herren utstrekke fra Sion! hersk midt iblandt dine fiender!
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Ditt folk møter villig frem på ditt veldes dag; i hellig prydelse kommer din ungdom til dig, som dugg ut av morgenrødens skjød.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 Herren har svoret, og han skal ikke angre det: Du er prest evindelig efter Melkisedeks vis.
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 Herren ved din høire hånd knuser konger på sin vredes dag.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 Han holder dom iblandt hedningene, fyller op med lik, knuser hoder over den vide jord.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 Av bekken drikker han på veien, derfor løfter han høit sitt hode.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< Salmenes 110 >