< Lukas 14 >

1 Og det skjedde da han kom inn i en av de øverste fariseeres hus på en sabbat for å holde måltid, og de lurte på ham,
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 se, da var der en vattersottig mann like for ham.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 Og Jesus tok til orde og talte til de lovkyndige og fariseerne og sa: Er det tillatt å helbrede på sabbaten, eller ikke?
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 Men de tidde. Og han tok på ham og helbredet ham, og lot ham gå.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 Og han tok atter til orde og sa til dem: Hvem av eder har en sønn eller en okse som faller i en brønn, og drar dem ikke straks op igjen på sabbatsdagen?
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 Men de var ikke i stand til å svare ham på dette.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 Og han sa en lignelse til gjestene, da han la merke til hvorledes de valgte sig ut de øverste seter:
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 Når du blir buden av nogen til bryllups, da sett dig ikke øverst ved bordet, forat ikke en gjævere enn du skal være buden,
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 og den som innbød dig og ham, skal komme og si til dig: Gi denne mann rum! og du så med skam skal komme til å sitte nederst.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Men når du er buden, da gå og sett dig nederst, forat han som innbød dig, kan si til dig når han kommer: Venn, kom hit, sett dig høiere op! Da får du ære i alle deres øine som sitter til bords med dig;
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 for hver den sig selv ophøier, skal fornedres, og den sig selv fornedrer, skal ophøies.
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 Han sa også til den som hadde innbudt ham: Når du gjør gjestebud middag eller aften, da innbyd ikke dine venner eller dine brødre eller dine frender eller rike granner, forat ikke de skal be dig igjen, så du får gjengjeld!
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 Men når du gjør gjestebud, da be fattige, vanføre, halte, blinde!
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 så er du salig; for de har ikke noget å gi dig igjen, men du skal få det igjen i de rettferdiges opstandelse.
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 Da en av dem som satt med til bords, hørte dette, sa han til ham: Salig er den som får sitte til bords i Guds rike.
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 Da sa han til ham: Det var en mann som gjorde en stor nattverd og innbød mange;
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 og han sendte sin tjener ut ved den tid nattverden skulde holdes, for å si til de innbudne: Kom! for nu er det ferdig.
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 Men de begynte alle som én å undskylde sig. Den første sa til ham: Jeg har kjøpt en aker og må nødvendig gå ut og se på den; jeg ber dig, ha mig undskyldt!
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 Og en annen sa: Jeg har kjøpt fem par okser og går ut for å prøve dem; jeg ber dig, ha mig undskyldt!
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 Og atter en annen sa: Jeg har tatt mig en hustru, og derfor kan jeg ikke komme.
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 Og tjeneren kom og fortalte sin herre dette. Da blev husbonden harm og sa til tjeneren: Gå i hast ut på byens gater og streder, og før herinn de fattige og vanføre og blinde og halte!
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 Og tjeneren sa: Herre! det er gjort som du bød, og der er ennu rum.
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 Da sa herren til tjeneren: Gå ut på veiene og ved gjerdene og nød dem til å komme inn, forat mitt hus kan bli fullt!
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 For jeg sier eder at ingen av de menn som var innbudt, skal smake min nattverd.
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Og meget folk vandret sammen med ham. Og han vendte sig og sa til dem:
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 Om nogen kommer til mig og ikke hater sin far og mor og hustru og barn og brødre og søstre, ja endog sitt eget liv, han kan ikke være min disippel.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 Og den som ikke bærer sitt kors og følger efter mig, han kan ikke være min disippel.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 For hvem av eder som vil bygge et tårn, setter sig ikke først ned og regner efter hvad det vil koste, om han har nok til å fullføre det med,
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 forat ikke, når han har lagt grunnen og ikke er i stand til å fullføre det, alle de som ser det, skal begynne å spotte ham og si:
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 Denne mann begynte å bygge, og var ikke i stand til å fullføre det?
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 Eller hvilken konge som drar ut for å møte en annen konge i strid, setter sig ikke først ned og rådslår om han med ti tusen er i stand til å møte den som kommer imot ham med tyve tusen?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 Men kan han ikke det, da skikker han sendemenn til ham, mens han ennu er langt borte, og tinger om fred.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 Således kan da ingen av eder være min disippel uten at han opgir alt det han eier.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 Salt er en god ting, men når også saltet mister sin kraft, hvad skal det da saltes med?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 Det duer hverken i jord eller i gjødsel; det blir kastet ut. Den som har ører å høre med, han høre!
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Lukas 14 >