< Lukas 10 >

1 Siden utvalgte Herren også sytti andre og sendte dem ut, to og to, i forveien for sig til hver by og hvert sted hvor han selv skulde komme.
Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
2 Og han sa til dem: Høsten er stor, men arbeiderne få; bed derfor høstens herre at han vil drive arbeidere ut til sin høst!
Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
3 Gå avsted! Se, jeg sender eder som lam midt iblandt ulver.
Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
4 Bær ikke pung, ikke skreppe, ikke sko; gi eder ikke i tale med nogen på veien!
Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
5 Men hvor I kommer inn i et hus, der skal I først si: Fred være med dette hus!
“Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
6 Og er det et fredens barn der, da skal eders fred hvile over ham, men hvis ikke, da skal den vende tilbake over eder.
In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
7 Men bli der i huset, og et og drikk hvad de byr eder! for arbeideren er sin lønn verd. I skal ikke flytte fra hus til hus.
Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
8 Og hvor I kommer inn i en by og de tar imot eder, der skal I ete hvad de setter frem for eder,
“Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
9 og helbred de syke som er der, og si til dem: Guds rike er kommet nær til eder!
Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
10 Men hvor I kommer inn i en by og de ikke tar imot eder, der skal I gå ut på dens gater og si:
Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
11 Endog støvet som er blitt hengende ved våre føtter av eders by, stryker vi av til eder; men dette skal I vite at Guds rike er kommet nær!
‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
12 Jeg sier eder at det skal gå Sodoma tåleligere på hin dag enn den by.
Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
13 Ve dig, Korasin! ve dig, Betsaida! for dersom de kraftige gjerninger som er gjort i eder, var gjort i Tyrus og Sidon, da hadde de for lenge siden omvendt sig og sittet i sekk og aske.
“‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
14 Dog, det skal gå Tyrus og Sidon tåleligere i dommen enn eder.
A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
15 Og du, Kapernaum, som er blitt ophøiet like til himmelen! like til dødsriket skal du bli nedstøtt. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs g86)
16 Den som hører eder, hører mig, og den som forkaster eder, forkaster mig, og den som forkaster mig, forkaster ham som sendte mig.
“Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
17 Og de sytti kom glade tilbake og sa: Herre! endog de onde ånder er oss lydige i ditt navn!
Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
18 Da sa han til dem: Jeg så Satan falle ned fra himmelen som et lyn.
Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
19 Se, jeg har gitt eder makt til å trede på slanger og skorpioner og over alt fiendens velde, og ingen ting skal skade eder;
Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
20 dog, gled eder ikke over dette at åndene er eder lydige, men gled eder over at eders navn er opskrevet i himmelen!
Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
21 I den samme stund frydet han sig i den Hellige Ånd og sa: Jeg priser dig, Fader, himmelens og jordens herre, fordi du har skjult dette for de vise og forstandige og åpenbaret det for de umyndige; ja, Fader, fordi således skjedde det som var velbehagelig for dig.
A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
22 Alle ting er mig overgitt av min Fader, og ingen kjenner til hvem Sønnen er, uten Faderen, og hvem Faderen er, uten Sønnen og den som Sønnen vil åpenbare det for.
“Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
23 Og han vendte sig særlig til sine disipler og sa: Salige er de øine som ser det I ser;
Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
24 for jeg sier eder: Mange profeter og konger har villet se det I ser, og har ikke fått se det, og høre det I hører, og har ikke fått høre det.
Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
25 Og se, en lovkyndig stod op og fristet ham og sa: Mester! hvad skal jeg gjøre forat jeg kan arve evig liv? (aiōnios g166)
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
26 Han sa til ham: Hvad er skrevet i loven? hvorledes leser du?
Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
27 Han svarte og sa: Du skal elske Herren din Gud av alt ditt hjerte og av all din sjel og av all din makt og av all din hu, og din næste som dig selv.
Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
28 Da sa han til ham: Du svarte rett; gjør dette, så skal du leve!
Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
29 Men da han vilde gjøre sig selv rettferdig, sa han til Jesus: Hvem er da min næste?
Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
30 Jesus svarte og sa: En mann gikk ned fra Jerusalem til Jeriko, og han falt iblandt røvere, som både klædde ham av og slo ham og gikk bort og lot ham ligge halvdød.
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
31 Men det traff sig så at en prest drog samme vei ned, og han så ham, og gikk like forbi.
Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
32 Likeså en levitt; han kom til stedet, gikk frem og så ham, og gikk like forbi.
Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
33 Men en samaritan som var på reise, kom dit hvor han var, og da han så ham, ynkedes han inderlig,
Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
34 og han gikk bort til ham og forbandt hans sår og helte olje og vin i dem, og han løftet ham op på sitt eget dyr og førte ham til et herberge og pleide ham.
Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
35 Og da det led mot næste dag, tok han to penninger frem og gav verten og sa til ham: Plei ham! og hvad mere du måtte koste på ham, det skal jeg betale dig igjen når jeg kommer tilbake.
Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
36 Hvem av disse tre synes du nu viste sig som den manns næste som var falt iblandt røverne?
“A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
37 Han sa: Den som gjorde barmhjertighet imot ham. Da sa Jesus til ham: Gå du bort og gjør likeså!
Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
38 Og det skjedde mens de var på vandring, at han kom til en by, og en kvinne ved navn Marta tok imot ham i sitt hus.
Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 Og hun hadde en søster som hette Maria; hun satte sig ved Jesu føtter og hørte på hans ord.
Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
40 Men Marta hadde det meget travelt med å tjene ham; hun gikk da frem og sa: Herre! bryr du dig ikke om at min søster har latt mig bli alene om å tjene dig? Si da til henne at hun skal hjelpe mig!
Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
41 Men Jesus svarte og sa til henne: Marta! Marta! du gjør dig strev og uro med mange ting;
Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
42 men ett er nødvendig. Maria har valgt den gode del, som ikke skal tas fra henne.
Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”

< Lukas 10 >