< Lukas 1 >

1 Eftersom mange har tatt sig fore å sette op en fortelling om de ting som er fullbyrdet iblandt oss,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 således som de som fra først av var øienvidner og blev ordets tjenere, har overgitt oss det,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 så har også jeg foresatt mig, efterat jeg nøie har gransket alt sammen fra først av, å nedskrive det i sammenheng for dig, gjæveste Teofilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 forat du kan lære å kjenne hvor pålitelige de lærdommer er som du er oplært i.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 I de dager da Herodes var konge i Jødeland, var det en prest ved navn Sakarias, av Abias skifte, og han hadde en hustru av Arons døtre, og hennes navn var Elisabet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 De var begge rettferdige for Gud, og vandret ulastelig i alle Herrens bud og forskrifter.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Og de hadde ikke barn; for Elisabet var ufruktbar, og de var begge kommet langt ut i årene.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Men det skjedde mens han gjorde prestetjeneste for Gud, da raden var kommet til hans skifte,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 at det efter preste-tjenestens sedvane tilfalt ham å gå inn i Herrens tempel og ofre røkelse;
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 og hele folkemengden stod utenfor og bad i røkofferets stund.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Da åpenbarte en Herrens engel sig for ham og stod på høire side av røkoffer-alteret.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Og da Sakarias så ham, blev han forferdet, og frykt falt på ham.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Men engelen sa til ham: Frykt ikke, Sakarias! din bønn er hørt, og din hustru Elisabet skal føde dig en sønn, og du skal kalle ham Johannes;
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 og han skal bli dig til glede og fryd, og mange skal glede sig over hans fødsel.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For han skal være stor for Herren, og han skal ikke drikke vin og sterk drikk, og han skal fylles med den Hellige Ånd like fra mors liv;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 og han skal omvende mange av Israels barn til Herren deres Gud,
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 og han skal gå i forveien for ham i Elias' ånd og kraft, for å vende fedres hjerter til barn og ulydige til rettferdiges sinnelag, for å berede Herren et velskikket folk.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Og Sakarias sa til engelen: Hvorav skal jeg vite dette? Jeg er jo en gammel mann, og min hustru er langt ute i årene.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Og engelen svarte ham: Jeg er Gabriel, som står for Guds åsyn, og jeg er utsendt for å tale til dig og forkynne dig dette glade budskap;
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 og se, du skal bli målløs, og ikke kunne tale før den dag da dette skjer, fordi du ikke trodde mine ord, som skal fullbyrdes i sin tid.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Og folket stod og ventet på Sakarias, og de undredes over at han blev så lenge i templet.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Men da han kom ut, kunde han ikke tale til dem, og de skjønte at han hadde sett et syn i templet, og han nikket til dem, og var og blev stum.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Og det skjedde da hans tjenestedager var til ende, da drog han hjem til sitt hus.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Men efter disse dager blev hans hustru Elisabet fruktsommelig, og hun trakk sig tilbake i ensomhet i fem måneder, og sa:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Så har Herren gjort med mig i de dager da han så til mig for å bortta min vanære iblandt menneskene.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Men i den sjette måned blev engelen Gabriel sendt fra Gud til en by i Galilea som heter Nasaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 til en jomfru som var trolovet med en mann ved navn Josef, av Davids hus, og jomfruens navn var Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Og engelen kom inn til henne og sa: Vær hilset, du benådede! Herren er med dig; velsignet er du blandt kvinner!
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Men hun blev forferdet over hans ord, og grundet på hvad dette skulde være for en hilsen.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Og engelen sa til henne: Frykt ikke, Maria! for du har funnet nåde hos Gud;
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 og se, du skal bli fruktsommelig og føde en sønn, og du skal kalle ham Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Han skal være stor og kalles den Høiestes Sønn, og Gud Herren skal gi ham hans far Davids trone,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 og han skal være konge over Jakobs hus evindelig, og det skal ikke være ende på hans kongedømme. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Men Maria sa til engelen: Hvorledes skal dette gå til, da jeg ikke vet av mann?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Og engelen svarte henne: Den Hellige Ånd skal komme over dig, og den Høiestes kraft skal overskygge dig; derfor skal også det hellige som fødes, kalles Guds Sønn.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Og se, Elisabet, din slektning, har også undfanget en sønn i sin alderdom, og hun, som kaltes ufruktbar, er nu i sin sjette måned.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For ingen ting er umulig for Gud.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Da sa Maria: Se, jeg er Herrens tjenerinne; mig skje efter ditt ord! Og engelen skiltes fra henne.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Men Maria stod op i de dager og skyndte sig til fjellbygdene, til en by i Juda,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 og hun kom inn i Sakarias' hus og hilste på Elisabet.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Og det skjedde da Elisabet hørte Marias hilsen, da sprang fosteret i hennes liv, og Elisabet blev fylt med den Hellige Ånd
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 og ropte med høi røst og sa: Velsignet er du blandt kvinner, og velsignet er ditt livs frukt!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Og hvorledes times mig dette, at min Herres mor kommer til mig?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For se, da lyden av din hilsen nådde mitt øre, sprang fosteret i mitt liv med fryd.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Og salig er hun som trodde; for fullbyrdes skal det som er sagt henne av Herren.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Da sa Maria: Min sjel ophøier Herren,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 og min ånd fryder sig i Gud, min frelser,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 han som har sett til sin tjenerinnes ringhet. For se, fra nu av skal alle slekter prise mig salig,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 fordi han har gjort store ting imot mig, han, den mektige, og hellig er hans navn,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 og hans miskunn er fra slekt til slekt over dem som frykter ham.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Han gjorde veldig verk med sin arm, han adspredte dem som var overmodige i sitt hjertes tanke;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 han støtte stormenn fra deres høiseter og ophøiet de små;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 hungrige mettet han med gode gaver, og rikmenn lot han gå bort med tomme hender.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Han tok sig av Israel, sin tjener, for å komme miskunn i hu
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 - således som han talte til våre fedre - mot Abraham og hans ætt til evig tid. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Og Maria blev hos henne omkring tre måneder, og vendte så hjem igjen til sitt hus.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Men for Elisabet kom tiden da hun skulde føde, og hun fødte en sønn,
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 og hennes granner og frender fikk høre at Herren hadde gjort sin miskunn stor mot henne, og de gledet sig med henne.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Og det skjedde på den åttende dag, da kom de for å omskjære barnet, og de vilde kalle ham Sakarias efter hans far.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Da tok hans mor til orde og sa: Nei, han skal hete Johannes.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Og de sa til henne: Men det er jo ingen i din ætt som har dette navn.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 De gjorde da tegn til hans far for å få vite hvad han vilde han skulde hete.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Og han bad om en tavle og skrev disse ord: Johannes er hans navn. Og de undret sig alle.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Men straks blev hans munn oplatt og hans tunge løst, og han talte og lovet Gud.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Og det kom frykt på alle dem som bodde deromkring, og i alle Judeas fjellbygder talte de med hverandre om alle disse ting,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 og alle som hørte det, la det på hjerte og sa: Hvad skal det da bli av dette barn? For Herrens hånd var med ham.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Og hans far Sakarias blev fylt med den Hellige Ånd og talte profetiske ord og sa:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Lovet være Herren, Israels Gud, han som så til sitt folk og forløste det!
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Og han opreiste oss et frelsens horn i sin tjener Davids hus,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 således som han talte gjennem sine hellige profeters munn fra fordums tid av, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 en frelse fra våre fiender og fra alle deres hånd som hater oss,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 for å gjøre miskunn mot våre fedre og komme sin hellige pakt i hu,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 den ed han svor Abraham, vår far,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 for å fri oss av våre fienders hånd og gi oss å tjene ham uten frykt
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 i hellighet og rettferdighet for hans åsyn alle våre dager.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Men også du, barn, skal kalles den Høiestes profet; for du skal gå frem for Herrens åsyn for å rydde hans veier,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 for å lære hans folk frelse å kjenne ved deres synders forlatelse
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 for vår Guds miskunnelige hjertelags skyld, som lot solopgang fra det høie gjeste oss,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 for å lyse for dem som sitter i mørke og dødsskygge, for å styre våre føtter inn på fredens vei.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Men barnet vokste og blev sterkt i ånden, og han var i ødemarkene til den dag da han blev ført frem for Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Lukas 1 >