< Josvas 6 >

1 Jeriko holdt sine porter stengt og var fast tillukket for Israels barns skyld; ingen gikk ut, og ingen kom inn.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 Da sa Herren til Josva: Se, jeg har gitt Jeriko med kongen og de djerve stridsmenn i din hånd.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 La nu alle krigsmennene gå omkring byen, rundt om den én gang! Således skal du gjøre i seks dager;
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 og syv prester skal bære syv larmbasuner foran arken; men den syvende dag skal I gå syv ganger omkring byen, og prestene skal støte i basunene.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Og når de blåser i larmhornet med lange toner, og I hører basunklangen, skal hele folket sette i et stort skrik; da skal byens mur falle ned der hvor den står, så folket kan stige inn over den, enhver rett frem for sig.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Da kalte Josva, Nuns sønn, prestene til sig og sa til dem: I skal bære paktens ark, og syv prester skal bære syv larmbasuner foran Herrens ark.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 Og til folket sa han: Dra frem og gå omkring byen, og de væbnede menn skal dra frem foran Herrens ark.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 Da Josva hadde sagt dette til folket, gikk de frem de syv prester som bar de syv larmbasuner for Herrens åsyn; de støtte i basunene, og Herrens pakts-ark fulgte efter dem.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 Og de væbnede menn gikk foran prestene som støtte i basunene, og de som endte toget, gikk efter arken, mens der ustanselig støttes i basunene.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 Og Josva bød folket og sa: I skal ikke opløfte hærrop og ikke la eders røst høre; det skal ikke gå et ord ut av eders munn før den dag jeg sier til eder: Rop nu! Da skal I rope.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 Så gikk Herrens ark omkring byen, rundt om den, én gang; derefter drog de inn i leiren og blev der natten over.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 Morgenen efter stod Josva tidlig op, og prestene bar Herrens ark.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 Og de syv prester som bar de syv larmbasuner foran Herrens ark, gikk og støtte ustanselig i basunene, og de væbnede menn gikk foran dem, og de som endte toget, gikk efter Herrens ark, mens der ustanselig støttes i basunene.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 Således gikk de den annen dag én gang omkring byen og vendte så tilbake til leiren; dette gjorde de i seks dager.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 Den syvende dag stod de tidlig op, med det samme det tok til å dages, og gikk syv ganger omkring byen; de bar sig at på samme vis som før, bare at de denne dag gikk syv ganger omkring byen.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 Og da prestene den syvende gang støtte i basunene, da sa Josva til folket: Rop nu! For Herren har gitt eder byen.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 Og byen med alt det som i den er, skal være vidd til Herren og bannlyst, bare skjøgen Rahab skal få leve, med alle som er i huset hos henne, fordi hun skjulte de menn vi hadde utsendt.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 Men ta eder vel i vare for det som er bannlyst, at I ikke først slår med bann og så tar av det som er bannlyst, og således legger Israels leir under bann og fører den i ulykke.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 Men alt sølv og gull og alle ting som er av kobber og jern, skal være helliget til Herren og komme i Herrens skattkammer.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Så ropte folket, og de støtte i basunene; og det skjedde da folket hørte basunklangen, og de satte i et stort skrik, da falt muren helt sammen, og folket steg bent inn i byen og inntok den.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 Og de slo alt det som var i byen, med bann; både menn og kvinner, både unge og gamle, storfe og småfe og asener slo de med sverdets egg.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 Men til de to menn som hadde utspeidet landet, sa Josva: Gå inn i skjøgens hus og før kvinnen og alle dem som hører henne til, ut derfra, således som I har tilsvoret henne.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 De unge menn som hadde vært speidere, gikk da inn og førte Rahab ut av huset og likeså hennes far og mor og brødre og alle som hørte henne til; hele hennes slekt førte de ut og lot dem få opholde sig et sted utenfor Israels leir.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Men byen med alt det som i den var, brente de op med ild; bare sølvet og gullet og alle ting som var av kobber og jern, la de ned i skattkammeret i Herrens hus.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Men skjøgen Rahab og hennes fars slekt og alle dem som hørte henne til, lot Josva leve; hun blev boende blandt Israels folk inntil denne dag, fordi hun skjulte de menn som Josva hadde sendt for å utspeide Jeriko.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 Dengang lot Josva folket sverge denne ed: Forbannet for Herrens åsyn være den mann som tar sig fore å bygge op igjen denne by Jeriko! Når han legger dens grunnvoll, skal det koste ham hans førstefødte sønn, og når han setter op dens porter, skal det koste ham hans yngste.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 Og Herren var med Josva, og ryktet om ham kom ut over hele landet.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.

< Josvas 6 >