< Jobs 37 >

1 Ja, over dette forferdes mitt hjerte og hopper i mitt bryst.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Hør, hør braket av hans røst og det drønn som går ut av hans munn!
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Under hele himmelen lar han det fare, og han sender sitt lys til jordens ytterste ender.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Efterpå brøler røsten, han tordner med sin veldige røst; han holder ikke lynene tilbake når hans røst lar sig høre.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Gud tordner underfullt med sin røst; han gjør storverk, og vi forstår dem ikke.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Han sier til sneen: Fall til jorden! - og likeså til skyllregnet, sitt sterke skyllregn.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Hvert menneskes hånd forsegler han, forat alle mennesker som han har skapt, må komme til å kjenne ham.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Da går de ville dyr inn i sine huler, og de holder sig i sine hi.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Fra Sydens innerste kammer kommer storm, og med nordenvinden kommer kulde.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Av Guds ånde kommer is, og brede vann bindes.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Med væte fyller han skyen, og han spreder sine lynskyer,
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 og de svinger hit og dit, efter som han leder dem, forat de skal utføre alt det han byder dem, over den vide jord;
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 enten til tukt, når det er til gagn for hans jord, eller til velsignelse lar han dem komme.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Vend ditt øre til dette, Job! Stå stille og gi akt på Guds under!
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Forstår du hvorledes Gud styrer dem og lar sine skyers lyn blinke frem?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Forstår du hvorledes skyene svever om i luften, forstår du den Allvitendes under,
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 du hvis klær blir varme når jorden ligger og dormer i sønnenvind?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Kan du med ham spenne ut himmelen, så fast som et speil av støpt metall?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Lær oss hvad vi skal si til ham! Vi kan ikke fremføre noget for bare mørke.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Skal det fortelles ham at jeg vil tale med ham? Har nogen sagt at han ønsker sin egen undergang?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Og nu, menneskene ser ikke lyset, enda det skinner klart på himmelen, og en vind er faret frem og har renset den.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Fra Norden kommer gull; om Gud er der en forferdende herlighet.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Den Allmektige finner vi ikke, han som er så stor i makt; men retten og den strenge rettferdighet krenker han ikke.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Derfor frykter menneskene ham; men han enser ikke nogen selvklok mann.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Jobs 37 >