< Jobs 34 >

1 Og Elihu tok atter til orde og sa:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Hør mine ord, I vise, og lån mig øre, I forstandige!
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Øret prøver jo ord, likesom ganen smaker mat.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 La oss velge det som er rett; la oss sammen søke å finne ut hvad der er godt!
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Job har jo sagt: Jeg er rettferdig, og Gud har tatt min rett fra mig;
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 tross min rett skal jeg være en løgner; en drepende pil har rammet mig, enda der ingen brøde er hos mig.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Hvem er en mann som Job, han som drikker bespottelse som vann
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 og gir sig i lag med dem som gjør ondt, og søker omgang med ugudelige menn?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For han har sagt: En mann har intet gagn av at han holder vennskap med Gud.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Derfor, I forstandige, hør på mig! Det være langt fra Gud å gjøre noget syndig og fra den Allmektige å være urettferdig!
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Han lønner mennesket efter dets gjerninger og gjengjelder mannen efter hans ferd.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Ja sannelig, Gud gjør ikke noget syndig, og den Allmektige forvender ikke retten.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Hvem har overgitt jorden til hans varetekt, og hvem har overlatt hele jorderike til ham?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Dersom han bare vilde tenke på sig selv og dra sin Ånd og sin ånde til sig igjen,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 da skulde alt kjød opgi ånden på én gang, og mennesket bli til støv igjen.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Men gi nu akt og hør på dette, lytt nøye til mine ord!
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Kan vel en som hater retten, være hersker? Eller tør du fordømme den Rettferdige, den Mektige?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Sier vel nogen til en konge: Din niding, eller til en fyrste: Du ugudelige?
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Gud tar jo ikke parti for fyrster og akter ikke en rik høiere enn en fattig? De er jo alle hans henders verk.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 I et øieblikk dør de, midt om natten; folket raver og forgår, og den mektige rykkes bort, ikke ved menneskehånd.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For hans øine vokter på hver manns veier, og han ser alle hans skritt;
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 det finnes intet mørke og ingen dødsskygge hvor de som gjør ondt kan skjule sig;
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Gud har ikke nødig å gi lenge akt på en mann før han må møte for Guds dom.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Han knuser de mektige uten å granske deres sak og setter så andre i deres sted.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Ja, han kjenner deres gjerninger, og han slår dem ned om natten så de går til grunne.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Han tukter dem som ugjerningsmenn, på et sted hvor alle kan se det;
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 for derfor vek de bort fra ham og aktet ikke på nogen av hans veier,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 forat de skulde la de fattiges skrik komme for ham, forat han skulde høre de undertryktes rop.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Lar han være å skride inn, hvem tør da fordømme ham? Skjuler han sitt åsyn, hvem får da se ham? Både med et folk og med et enkelt menneske gjør han jo således,
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 forat et gudløst menneske ikke skal herske, forat det ikke skal være snarer for folket.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 For har vel et slikt menneske nogensinne sagt til Gud: Jeg har vært overmodig, jeg vil herefter ikke gjøre det som ondt er;
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 det jeg ikke ser, det må du lære mig; har jeg gjort urett, så vil jeg ikke gjøre det mere?
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Skulde han vel gjengjelde efter ditt tykke? Du har jo klandret ham. Så må du velge og ikke jeg, og hvad du vet, får du si.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Forstandige menn vil si til mig, ja hver vismann som hører på mig:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job taler uten skjønnsomhet, og hans ord er ikke forstandige.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Gid Job måtte bli prøvd uavlatelig, fordi han har svart på onde menneskers vis!
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For til sin synd legger han brøde; her iblandt oss klapper han i hendene og bruker mange ord om Gud.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Jobs 34 >