< Jobs 27 >

1 Og Job blev ved å fremføre sin visdomstale og sa:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 Så sant Gud lever, som har tatt min rett fra mig, den Allmektige, som har voldt mig bitter sorg
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 - for ennu er hele mitt livspust i mig og den Allmektiges ånde i min nese -:
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Mine leber taler ikke urett, og min tunge taler ikke svik.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Det være langt fra mig å gi eder rett! Inntil jeg opgir ånden, lar jeg ikke min brødefrihet tas fra mig.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Jeg holder fast på min rettferdighet og slipper den ikke; mitt hjerte laster mig ikke for nogen av mine dager.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 La min fiende stå der som en ugudelig, og min motstander som en urettferdig!
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 For hvad håp har den gudløse, når Gud avskjærer hans liv, når han tar hans sjel fra ham?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Hører vel Gud hans skrik når trengsel kommer over ham?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Eller kan han glede sig i den Allmektige, kan han påkalle Gud til enhver tid?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Jeg vil lære eder om Guds hånd; jeg vil ikke dølge hvad den Allmektige har i sinne.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 I har jo alle selv sett det; hvorfor fører I da så tom en tale?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Dette er det ugudelige menneskes lodd hos Gud og den arv som voldsmennene får av den Allmektige:
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Får han mange barn, så er de hjemfalt til sverdet; hans ætlinger får ikke brød å mette sig med.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 De av dem som slipper unda, legges i graven ved pest, og enkene holder ikke sørgefest over dem.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Når han dynger op sølv som støv og samler sig klær som lere,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 så blir det de rettferdige som klær sig med det han har samlet, og sølvet skal de skyldfrie dele.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Som møllet har han bygget sitt hus og som den hytte en markvokter lager sig.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Rik legger han sig, og intet er tatt bort; han slår sine øine op, og det er der ikke.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Som en vannflom innhenter redsler ham, om natten fører en storm ham bort.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Østenvinden løfter ham op, så han farer avsted, og den blåser ham bort fra hans sted.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Gud skyter sine piler mot ham og sparer ham ikke; for hans hånd flyr han i hast.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Folk klapper i hendene og håner ham og piper ham bort fra hans sted.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Jobs 27 >