< Jeremias 46 >

1 Dette er Herrens ord som kom til profeten Jeremias om hedningefolkene.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Om Egypten. Om egypterkongen Farao Nekos hær, som stod ved elven Eufrat, ved Karkemis, og som Babels konge Nebukadnesar slo i Judas konge Jojakims, Josias' sønns fjerde år:
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 Sett skjoldene i stand, de små og de store, og rykk frem til striden!
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Spenn hestene for og sitt op, I ryttere, og still eder op med hjelmer på! Gjør spydene blanke, ta brynene på!
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 Hvorfor ser jeg dem forferdet vike tilbake? Og deres kjemper blir slått og tar flukten uten å vende sig om; redsel er det rundt omkring, sier Herren.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 Den lette skal ikke undfly, og kjempen ikke undslippe; mot nord, ved bredden av elven Eufrat, snubler de og faller.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 Hvem er det som stiger op lik Nilen, hvis vann bølger som strømmene?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 Egypten stiger op som Nilen, og dets vann bølger som strømmene; det sier: Jeg vil stige op og dekke landene, jeg vil ødelegge byer og dem som bor i dem.
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Far frem, I hester, og ras avsted, I vogner! Kjempene skal rykke ut, etiopere og puteere, som fører skjold, og menn fra Lud, som fører og spenner bue.
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 Men den dag er for Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, en hevnens dag, til hevn over hans fiender, og sverdet skal fortære og mettes og bli drukkent av deres blod; for en offerslakting holder Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, i landet i nord ved elven Eufrat.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Dra op til Gilead og hent balsam, du jomfru, Egyptens datter! Forgjeves bruker du mange slags lægedom; det finnes ikke plaster for dig.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 Folkeslag hører om din skam, og jorden er full av ditt skrik; for den ene stridsmann snubler over den andre, de faller begge to.
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 Dette er det ord Herren talte til profeten Jeremias om at Babels konge Nebukadnesar skulde komme og slå Egyptens land:
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 Kunngjør det i Egypten, la det høres i Migdol og la det høres i Memfis og Tahpanhes! Si: Still dig frem og gjør dig ferdig! For sverdet har fortært alt rundt omkring dig.
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Hvorfor er din sterke styrtet til jorden? Han holdt ikke stand; for Herren støtte ham ned.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 Han får mange til å snuble, ja, den ene faller ovenpå den andre, og de sier: Op, la oss vende tilbake til vårt folk og vårt fødeland for det herjende sverd!
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 Da roper de: Farao, Egyptens konge, er ødelagt! Han lot den rette tid gå forbi.
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 Så sant jeg lever, sier kongen, han hvis navn er Herren, hærskarenes Gud: Som Tabor iblandt fjellene og som Karmel ved havet kommer han.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 Rust dig ut til å gå i landflyktighet, du Egyptens datter som bor i landet! For Memfis skal bli til en ørken og bli ødelagt, så ingen bor der.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 En herlig kvige er Egypten - kleggen fra nord kommer, den kommer.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Også de leide krigsmenn som det har i sin midte, de som er lik gjøkalver, ja, også de vender om, flyr alle sammen, de holder ikke stand; for deres ulykkesdag er kommet over dem, deres hjemsøkelses tid.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 Dets røst skal lyde som ormens; for med en hær drar de frem, og med økser kommer de mot det som tømmerhuggere.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 De hugger ned dets skog, sier Herren; for den er ugjennemtrengelig; de er flere enn gresshoppene, det er ikke tall på dem.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 Egyptens datter blir til skamme; hun blir gitt i hendene på et folk fra nord.
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud, sier: Se, jeg hjemsøker Amon fra No og Farao og Egypten og dets guder og dets konger, både Farao og dem som setter sin lit til ham,
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 og jeg gir dem i deres hånd som står dem efter livet, i Babels konge Nebukadnesars hånd og i hans tjeneres hånd; men derefter skal det få leve i ro som i fordums dager, sier Herren.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 Men frykt ikke, du min tjener Jakob, og reddes ikke, Israel! For se, jeg frelser dig fra det fjerne land og din ætt fra deres fangenskaps land, og Jakob skal vende tilbake og ha ro og være trygg, og ingen skal forferde ham.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 Frykt ikke, min tjener Jakob, sier Herren, for jeg er med dig; jeg vil gjøre ende på alle de folk som jeg har drevet dig bort til, men dig vil jeg ikke gjøre ende på; jeg vil tukte dig med måte; men helt ustraffet vil jeg ikke la dig være.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jeremias 46 >