< Esaias 1 >

1 Dette er de syner som Esaias, sønn av Amos, så om Juda og Jerusalem i de dager da Ussias, Jotam, Akas og Esekias var konger i Juda.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Hør, I himler, og lytt til, du jord! For Herren taler: Barn har jeg opfødd og fostret; men de er falt fra mig.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 En okse kjenner sin eiermann, og et asen sin herres krybbe; Israel kjenner intet, mitt folk forstår intet.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Ve det syndige folk, det folk med tung misgjerning, den yngel av ugjerningsmenn, de vanartede barn! De har forlatt Herren, har foraktet Israels Hellige, er veket fra ham.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 Hvorfor vil I la eder slå fremdeles? Hvorfor øker I eders frafall? Hvert hode er sykt, og hvert hjerte er svakt.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 Fra fotsåle til hode er der intet helt på det; sår, buler og friske slag! De er ikke klemt ut og ikke forbundet og ikke utbløtt med olje.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Eders land er en ørken, eders byer opbrent med ild; eders jord opetes av fremmede for eders øine, og en ørken er der, som efter fremmedes herjing.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 Bare Sions datter er blitt igjen som en løvhytte i en vingård, som en vekterhytte på en agurkmark, som en kringsatt by.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 Hadde ikke Herren, hærskarenes Gud, levnet oss en liten rest, da var vi som Sodoma, da lignet vi Gomorra.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Hør Herrens ord, I Sodomafyrster! Lytt til vår Guds lov, du Gomorra-folk!
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 Hvad skal jeg med eders mange slaktoffer? sier Herren; jeg er mett av brennoffer av værer og av gjøkalvers fett, og til blod av okser og lam og bukker har jeg ikke lyst.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 Når I kommer for å vise eder for mitt åsyn, hvem har da krevd dette av eder at I skal nedtrede mine forgårder?
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Kom ikke mere frem med tomt matoffer! Det er mig en vederstyggelig røkelse. Nymåne og sabbat, festlig forsamling - jeg tåler ikke høitid og urett sammen.
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 Eders nymåner og fester hater min sjel, de er blitt mig en byrde; jeg er trett av å bære dem.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 Og når I breder ut eders hender, skjuler jeg mine øine for eder; om I enn beder meget, hører jeg ikke; eders hender er fulle av blod.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Tvett eder, rens eder, ta eders onde gjerninger bort fra mine øine, hold op å gjøre det som er ondt!
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 Lær å gjøre det gode, legg vinn på det som er rett, vis voldsmannen på rett vei, hjelp den farløse til hans rett, før enkens sak!
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 Kom og la oss gå i rette med hverandre, sier Herren; om eders synder er som purpur, skal de bli hvite som sne; om de er røde som skarlagen, skal de bli som den hvite ull.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 Er I villige og hører, skal I ete landets gode ting,
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 men er I uvillige og gjenstridige, skal I bli opett av sverdet; for Herrens munn har talt.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 Hvor den er blitt til en horkvinne, den trofaste by, som var full av rett, hvor rettferd hadde hjemme, og nu - mordere!
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Ditt sølv er blitt til slagger, din vin blandet op med vann;
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 dine førere er oprørere og tyvers stallbrødre; enhver av dem elsker bestikkelse og jager efter gaver; den farløse hjelper de ikke til hans rett, og enkens sak tar de sig ikke av.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Derfor sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, Israels Veldige: Ve! Jeg vil kjøle min harme på mine motstandere og ta hevn over mine fiender.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 Og jeg vil igjen ta mig av dig og smelte ut dine slagger som med lutsalt og skille ut alt ditt bly.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 Og jeg vil atter gi dig slike dommere som i førstningen og rådsherrer som i begynnelsen; derefter skal du kalles rettferdighetens stad, en trofast by.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Sion skal forløses ved rett, og de omvendte der ved rettferdighet.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 Men undergang skal ramme alle overtredere og syndere, og de som forlater Herren, skal omkomme;
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 for de skal få skam av de eketrær som er eders lyst, og I skal bli til skamme ved de haver som I har så kjær;
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 for I skal bli som en ek med visne blad og som en have uten vann.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 Og den sterke skal bli til stry, og hans gjerning til en gnist, og de skal brenne begge tilsammen, og der er ingen som slukker.
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Esaias 1 >