< Esaias 28 >

1 Ve Efra'ims drukne menns stolte krone og den falmende blomst, hans fagre pryd, som troner over den fete dal, der de ligger drukne av vin.
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Se, Herren sender en som er sterk og veldig, lik en haglskur, en ødeleggende storm; som en flom av mektige, overstrømmende vann slår han alt til jorden med makt.
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 Med føtter skal den tredes ned, Efra'ims drukne menns stolte krone,
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 og med den falmende blomst, hans fagre pryd, som troner over den fete dal, skal det gå som med den fiken som er moden før sommeren er der: Så snart en ser den, sluker han den, mens den ennu er i hans hånd.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 På den tid skal Herren, hærskarenes Gud, være en fager krone og en herlig krans for resten av sitt folk,
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 og en doms ånd for den som sitter til doms, og styrke for dem som driver krigen tilbake til porten.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Men også de som er her, raver av vin og tumler av sterk drikk; prest og profet raver av sterk drikk, er overveldet av vin, tumler av sterk drikk; de raver i sine syner, vakler i sine dommer;
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 for alle bord er fulle av vemmelig spy, det finnes ikke en ren flekk.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 Hvem vil han lære kunnskap, og hvem vil han få til å forstå budskap? Er det barn som nettop er avvent fra melken, tatt bort fra brystet?
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 For bud på bud, bud på bud, regel på regel, regel på regel, litt her, litt der.
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 Ja, ved folk med stammende leber og i et annet tungemål skal han tale til dette folk,
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 han som sa til dem: Dette er ro, unn den mødige ro, og dette er hvile. Men de vilde ikke høre.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 Så skal da Herrens ord bli dem bud på bud, bud på bud, regel på regel, regel på regel, litt her, litt der, så de skal gå og falle baklengs og knuses og bindes og fanges.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 Derfor hør Herrens ord, I spottere, I som hersker over folket her i Jerusalem!
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 Fordi I sier: Vi har gjort en pakt med døden og et forbund med dødsriket; når den susende svepe farer frem, skal den ikke nå oss; for vi har gjort løgn til vår tilflukt og svik til vårt skjul - (Sheol h7585)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
16 derfor sier Herren, Israels Gud, så: Se, jeg har lagt i Sion en grunnsten, en prøvet sten, en kostelig, fast hjørnesten; den som tror, haster ikke.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 Og jeg vil gjøre rett til målesnor og rettferdighet til lodd, og hagl skal rive bort løgnens tilflukt, og skjulet skal vannene skylle bort.
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 Og eders pakt med døden skal slettes ut, og eders forbund med dødsriket skal ikke stå fast; når den susende svepe farer frem, da skal I bli trådt ned. (Sheol h7585)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
19 Hver gang den farer frem, skal den rive eder bort; hver morgen skal den fare frem, både dag og natt, og det skal være bare redsel å forstå budskapet;
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 for sengen er for kort til å strekke sig ut i, og teppet for smalt til å svøpe sig i.
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 For Herren skal reise sig likesom ved Perasim-fjellet, som i dalen ved Gibeon skal han vredes, for å gjøre sin gjerning? en underlig gjerning, og utrette sitt arbeid, et uhørt arbeid.
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 Og nu, spott ikke, forat ikke eders bånd skal bli strammet! For tilintetgjørelse og fast besluttet straffedom over hele jorden har jeg hørt fra Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Vend øret til og hør min røst, gi akt og hør min tale!
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Når plogmannen vil så, holder han da alltid på med å pløie, åpne og harve sin jord?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Når han har jevnet sin aker, spreder han da ikke ut dill og karve og sår hvete i rader og bygg på avmerket sted og spelt i kanten?
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 Hans Gud har vist ham den rette måte, han lærte ham det.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 For en tresker ikke dill med treskeslede, ruller heller ikke vognhjul over karve; men med stav banker en ut dill, og karve med kjepp.
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 Blir vel brødkorn knust? Nei, en tresker det ikke uavlatelig, og når en driver sine vognhjul og sine hester over det, knuser en det ikke.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 Også dette kommer fra Herren, hærskarenes Gud; han er underfull i råd, stor i visdom.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.

< Esaias 28 >