< Esaias 27 >

1 På den tid skal Herren med sitt sverd, det hårde og store og sterke, hjemsøke Leviatan, den lettfarende drage, og Leviatan, den buktede drage, og han skal drepe uhyret som er i havet.
A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
2 På den tid skal de synge: Der er en edel vingård; syng om den!
A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
3 Jeg, Herren, er dens vokter, hvert øieblikk vanner jeg den; forat ikke nogen skal hjemsøke den, vokter jeg den dag og natt.
Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
4 Vrede har jeg ikke mot den. Hadde jeg torner og tistler mot mig i krig, da vilde jeg gå løs på dem og brenne dem op alle sammen,
Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
5 dersom de da ikke skulde søke vern hos mig, gjøre fred med mig, ja, gjøre fred med mig.
Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
6 I de kommende dager skal Jakob skyte røtter, Israel blomstre og få skudd, og de skal fylle jorderike med frukt.
A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
7 Har vel Herren slått Israel så hårdt som han slo den som slo ham? Eller blev han drept således som hans fiender blev drept?
Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
8 Med måte gikk du i rette med folket da du jaget det fra dig. Herren drev det bort med sitt hårde vær på østenvindens dag.
Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
9 Derfor blir Jakobs misgjerning utsonet, og det at hans synd blir tatt bort, gir full frukt, når alle alterstener blir knust som kalkstener, og Astarte-billeder og solstøtter ikke reiser sig mere.
A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
10 For den faste by ligger forlatt, en folketom bolig, øde som ørkenen. Kalver beiter der; der hviler de og fortærer dens kvister;
Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
11 når dens grener blir tørre, brytes de av, kvinner kommer og gjør op ild med dem. For dette er ikke noget forstandig folk; derfor forbarmer dets skaper sig ikke over det, og han som dannet det, er ikke nådig mot det.
Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
12 Og det skal skje på den tid at Herren skal slå ned frukter like fra Storelven til Egyptens bekk, og I, Israels barn, I skal sankes op en for en.
A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
13 Og det skal skje på den tid at de skal støte i en stor basun, og da skal de komme de fortapte i Assurs land og de fordrevne i Egyptens land, og de skal tilbede Herren på det hellige berg i Jerusalem.
Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.

< Esaias 27 >