< Esaias 13 >

1 Utsagn om Babel, som Esaias, Amos' sønn, mottok i et syn.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Reis et banner på et bart fjell, rop høit til dem, vink med hånden at de kan dra inn gjennem voldsherrenes porter!
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 Jeg har opbudt mine innvidde menn og kalt mine helter til å tjene min vrede, mine stolte, jublende skarer.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Hør! Bulder på fjellene som av et stort folk! Hør! Brak av kongeriker, av sammenstrømmende folkeslag! Herren, hærskarenes Gud, mønstrer sin krigshær.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 De kommer fra et land langt borte, fra himmelens ende, Herren og hans vredes redskaper, for å ødelegge hele jorden.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Skrik og jamre eder! For Herrens dag er nær; den kommer som en ødeleggelse fra den Allmektige.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 Derfor blir alle hender slappe og hvert menneskehjerte smelter.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Og de forferdes; veer og smerter griper dem, som den fødende kvinne vrir de sig; fulle av redsel ser de på hverandre, deres ansikter blusser som ildsluer.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Se, Herrens dag kommer, fryktelig og full av harme og brennende vrede, for å gjøre jorden til en ørk og utslette dens syndere;
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 for himmelens stjerner og dens strålende stjernebilleder skal ikke la sitt lys skinne; solen er mørk når den går op, og månen skinner ikke.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 Jeg vil hjemsøke jorden for dens ondskap og de ugudelige for deres misgjerning, og jeg vil gjøre ende på de overmodiges stolthet og kue voldsmenns tross.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 Jeg vil gjøre folk sjeldnere enn fint gull og mennesker sjeldnere enn gull fra Ofir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 Derfor vil jeg ryste himmelen, og jorden skal beve og fare op fra sitt sted ved Herrens, hærskarenes Guds harme og på hans brennende vredes dag.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 Og det skal skje: Som et jaget rådyr, likesom får som ingen samler, skal de vende sig, hver til sitt folk, og fly hver til sitt land.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Hver den som treffes, skal gjennembores, og hver den som gripes, skal falle for sverdet.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Deres små barn skal knuses for deres øine; deres hus skal plyndres, og deres kvinner skjendes.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Se, jeg egger mot dem mederne, som ikke akter sølv og ikke har lyst til gull,
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 og deres buer feller guttene; over fosteret i mors liv forbarmer de sig ikke, med barn har deres øie ingen medynk.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Og med Babel, rikenes smykke, kaldeernes stolte pryd, skal det gå som da Gud omstyrtet Sodoma og Gomorra.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Det skal aldri mere reise sig igjen, og ingen skal bo der fra slekt til slekt; ingen araber skal slå op sitt telt der, og ingen hyrde la sin hjord hvile der.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Men ørkenens dyr skal hvile der, og dets hus skal være fulle av ugler, og strutser skal bo der, og raggete troll hoppe omkring der.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Og ville hunder skal tute i dets forlatte borger, og sjakaler i vellystens slotter. Snart kommer dets tid, og dets dager skal ikke forlenges.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Esaias 13 >