< Hoseas 9 >

1 Gled dig ikke, Israel, og juble ikke, likesom folkene! For du har forlatt din Gud i hor; du har elsket horelønn på hvert sted hvor kornet treskes.
Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
2 Treskeplassen og vinpersen skal ikke kunne fø dem, og mosten skal slå feil for dem.
Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
3 De skal ikke bli boende i Herrens land; men Efra'im skal vende tilbake til Egypten, og i Assur skal de ete det som er urent.
Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
4 De skal ikke ofre vin til drikkoffer for Herren, og deres slaktoffer skal ikke behage ham; som sorgens brød skal de være for dem; alle som eter det, skal bli urene; for sitt brød har de for sig selv, det kommer ikke i Herrens hus.
Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
5 Hvad vil I gjøre på høitidsdagen, på Herrens festdag?
Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
6 For de drar bort for ødeleggelses skyld; Egypten skal samle dem, Memfis begrave dem; deres sølvsmykker skal nesler ta i eie, torner skal vokse i deres telt.
Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
7 Kommet er hjemsøkelsens dager, kommet er gjengjeldelsens dager; Israel skal få merke det: En dåre er profeten, avsindig er åndens mann, fordi din misgjerning er så stor og ditt fiendskap så sterkt.
Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
8 Efra'im ser sig om efter andre guder ved siden av min Gud; profeten er en fuglefangersnare på alle hans veier, bare fiendskap i hans Guds hus.
Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
9 De er sunket dypt i fordervelse, som i Gibeas dager; han skal komme deres misgjerning i hu, han skal hjemsøke dem for deres synder.
Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
10 Som druer i ørkenen fant jeg Israel, som den tidligste frukt på et fikentre i dets første tid så jeg eders fedre; men da de kom til Ba'al-Peor, vidde de sig til avgudsdyrkelsen og blev vederstyggelige likesom den de elsket.
“Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
11 Efra'ims herlighet skal flyve bort som en fugl. Ingen fødsel, intet fruktsommelig morsliv, ingen undfangelse!
Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
12 Ja, selv om de opfør sine barn, vil jeg gjøre dem barnløse, så intet menneske blir tilbake; for ve dem når jeg forlater dem!
Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
13 Efra'im er, som om jeg så bort til Tyrus, plantet på en eng; men Efra'im må føre sine barn ut til bøddelen.
Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
14 Gi dem, Herre! - Ja, hvad skal du gi dem? Gi dem morsliv som føder i utide, og bryster som er uttørket!
Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
15 All deres ondskap er samlet i Gilgal, ja, der har jeg fattet hat til dem; for deres onde gjerningers skyld vil jeg drive dem ut av mitt hus; jeg vil ikke elske dem mere, alle deres førere er oprørere.
“Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
16 Efra'im er ormstukket, deres rot er blitt tørr, frukt skal de ikke bære; om de enn føder, vil jeg drepe deres dyre livsfrukt.
An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
17 Min Gud skal forkaste dem, fordi de ikke har hørt på ham, og de skal vanke om blandt folkene som flyktninger.
Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.

< Hoseas 9 >