< 1 Mosebok 30 >

1 Da Rakel så at hun og Jakob ikke fikk barn, blev hun misunnelig på sin søster og sa til Jakob: La mig få barn! Ellers dør jeg.
Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
2 Da optendtes Jakobs vrede mot Rakel, og han sa: Er jeg i Guds sted, som har nektet dig livsfrukt?
Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
3 Da sa hun: Se, der er min trælkvinne Bilha; gå inn til henne, forat hun kan føde på mine knær, så også jeg kan få barn ved henne!
Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
4 Så gav hun sin trælkvinne Bilha til hustru, og Jakob gikk inn til henne.
Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
5 Og Bilha blev fruktsommelig og fødte Jakob en sønn.
ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
6 Da sa Rakel: Gud har dømt i min sak; han har hørt min bønn og gitt mig en sønn. Derfor kalte hun ham Dan.
Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
7 Og Bilha, Rakels trælkvinne, blev atter fruktsommelig og fødte Jakob ennu en sønn.
Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
8 Da sa Rakel: Jeg har kjempet Guds kamper med min søster, og nu har jeg vunnet. Og hun kalte ham Naftali.
Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
9 Da Lea så at hun ikke fikk flere barn, tok hun sin trælkvinne Silpa og gav Jakob til hustru.
Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
10 Og Silpa, Leas trælkvinne, fødte Jakob en sønn.
Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
11 Da sa Lea: Til lykke! Og hun kalte ham Gad.
Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
12 Og Silpa, Leas trælkvinne, fødte Jakob ennu en sønn.
Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
13 Da sa Lea: Hvor lykkelig jeg er! For alle kvinner vil prise mig lykkelig. Og hun kalte ham Aser.
Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
14 En dag i hvetehøstens tid gikk Ruben ut og fant alruner på marken og bar dem hjem til Lea, sin mor; da sa Rakel til Lea: Kjære, gi mig nogen av din sønns alruner!
A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
15 Men hun svarte henne: Er det ikke nok at du har tatt min mann? Vil du nu også ta min sønns alruner? Da sa Rakel: Nu vel, han kan sove hos dig inatt, hvis jeg får din sønns alruner!
Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
16 Da Jakob om aftenen kom hjem fra marken, gikk Lea ham i møte og sa: Det er hos mig du skal være inatt; jeg har tinget dig for min sønns alruner. Så lå han hos henne den natt.
Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
17 Og Gud hørte Lea, og hun blev fruktsommelig og fødte Jakob en femte sønn.
Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
18 Da sa Lea: Gud har gitt mig min lønn, fordi jeg lot min mann få min trælkvinne. Og hun kalte ham Issakar.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
19 Og Lea blev atter fruktsommelig og fødte Jakob en sjette sønn.
Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
20 Da sa Lea: Gud har gitt mig en god gave; nu kommer min mann til å bo hos mig, for jeg har født ham seks sønner. Og hun kalte ham Sebulon.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
21 Siden fødte hun en datter og kalte henne Dina.
Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
22 Da kom Gud Rakel i hu, og Gud hørte henne og åpnet hennes morsliv.
Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
23 Hun blev fruktsommelig og fødte en sønn. Da sa hun: Gud har tatt bort min skam.
Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
24 Og hun kalte ham Josef og sa: Herren gi mig ennu en sønn!
Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
25 Da nu Rakel hadde født Josef, sa Jakob til Laban: La mig fare, så jeg kan dra hjem til mitt eget land!
Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
26 Gi mig mine hustruer og mine barn, som jeg har tjent dig for, så vil jeg dra bort; du vet jo selv hvorledes jeg har tjent dig.
Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
27 Da sa Laban til ham: Om du bare hadde nogen godhet for mig! Jeg er blitt varslet om at det er for din skyld Herren har velsignet mig.
Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
28 Så sa han: Si selv hvad du vil ha i lønn, så skal jeg gi dig det.
Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
29 Og Jakob sa til ham: Du vet selv hvorledes jeg har tjent dig, og hvad din buskap er blitt til under mine hender.
Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
30 For det var lite det du hadde før jeg kom, men nu har det øket til en stor mengde, og Herren har velsignet dig hvor jeg satte min fot. Men når skal jeg nu også få gjøre noget for mitt eget hus?
Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
31 Da sa Laban: Hvad skal jeg gi dig? Jakob svarte: Du skal ikke gi mig noget; dersom du vil gjøre som jeg nu sier, så skal jeg gjæte din buskap og vokte den, som jeg har gjort.
Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
32 Jeg vil idag gå gjennem hele din hjord og skille ut alt som er flekket og spraglet og alt som er sort blandt fårene, og likeså alt som er spraglet og flekket blandt gjetene; og det skal være min lønn.
Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
33 Og min ærlighet skal vidne for mig, når du siden engang kommer og ser over min lønn. Finnes det hos mig nogen gjet som ikke er flekket og spraglet, og noget får som ikke er sort, så er det stjålet.
Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
34 Da sa Laban: Vel, la det være som du har sagt!
Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
35 Og samme dag skilte han ut de stripete og spraglete gjetebukker og alle flekkete og spraglete gjeter, alt det som hadde noget hvitt på sig, og alt sort blandt fårene; og han lot sine sønner ta vare på det,
A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
36 og han la tre dagsreiser mellem sig og Jakob. Og Jakob gjætte resten av Labans småfe.
Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
37 Men Jakob tok sig friske kjepper av poppel-, hassel- og lønnetrær og skavde hvite striper på dem, så det hvite på kjeppene kom frem.
Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
38 Og han la kjeppene som han hadde skavd, i rennene - i vanntrauene, hvor småfeet kom for å drikke, like foran småfeet; for de parret sig når de kom for å drikke.
Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
39 Så parret småfeet sig ved kjeppene og fikk stripete, flekkete og spraglete unger.
sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
40 Men lammene skilte Jakob ut og lot småfeet vende øinene mot det stripete og alt det sorte blandt Labans småfe; og således fikk han sig hjorder for sig selv og slapp dem ikke sammen med Labans småfe.
Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
41 Og hver gang det sterke småfe parret sig, la Jakob kjeppene midt for øinene på dem i rennene, forat de skulde parre sig ved kjeppene;
A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
42 men når det var svakt småfe, la han ikke kjeppene der; således kom de svake til å tilhøre Laban og de sterke Jakob.
amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
43 Og mannen blev rikere og rikere, og han fikk meget småfe og trælkvinner og træler og kameler og asener.
Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.

< 1 Mosebok 30 >