< 1 Mosebok 22 >

1 Nogen tid derefter satte Gud Abraham på prøve, og han sa til ham: Abraham! Og han svarte: Ja, her er jeg.
Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
2 Da sa han: Ta din sønn, din eneste, ham som du har så kjær, Isak, og gå til Moria land og ofre ham der til brennoffer på et av fjellene, som jeg skal si dig!
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
3 Så stod Abraham tidlig op om morgenen og lesste på sitt asen og tok to av sine drenger med sig og Isak, sin sønn; han kløvde ved til brennofferet og gav sig på veien til det sted Gud hadde sagt ham.
Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
4 På den tredje dag, da Abraham så sig omkring, fikk han øie på stedet langt borte.
A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
5 Da sa Abraham til sine drenger: Bli I her med asenet! Jeg og gutten, vi vil gå dit bort og bede og så komme tilbake til eder.
Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
6 Så tok Abraham veden til brennofferet og la den på Isak, sin sønn, og selv tok han ilden og kniven i sin hånd; og så gikk de begge sammen.
Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
7 Da talte Isak til Abraham, sin far, og sa: Du far! Han svarte: Ja, min sønn! Han sa: Se, her er ilden og veden, men hvor er lammet til brennofferet?
sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
8 Abraham svarte: Gud skal selv utse sig lammet til brennofferet, min sønn! Så gikk de begge sammen.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
9 Og da de kom til det sted Gud hadde sagt ham, bygget Abraham et alter der og la veden til rette; så bandt han Isak, sin sønn, og la ham på alteret ovenpå veden.
Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
10 Og Abraham rakte ut hånden og tok kniven for å ofre sin sønn.
Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
11 Da ropte Herrens engel til ham fra himmelen og sa: Abraham, Abraham! - Han svarte: Ja, her er jeg.
Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
12 Da sa han: Legg ikke hånd på gutten og gjør ham ikke noget! For nu vet jeg at du frykter Gud, siden du ikke har spart din eneste sønn for min skyld.
Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
13 Da nu Abraham så op, fikk han se en vær bakenfor sig, som hang fast i buskene med sine horn; og Abraham gikk bort og tok væren og ofret den til brennoffer istedenfor sin sønn.
Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
14 Og Abraham kalte dette sted: Herren ser. Derfor sier folk den dag idag: På Herrens berg skal han la sig se.
Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
15 Og Herrens engel ropte ennu en gang til Abraham fra himmelen
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16 og sa: Ved mig selv sverger jeg, sier Herren: Fordi du gjorde dette og ikke sparte din eneste sønn,
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17 så vil jeg storlig velsigne dig og gjøre din ætt såre tallrik, som stjernene på himmelen og som sanden på havets bredd, og din ætt skal ta sine fienders porter i eie;
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18 og i din ætt skal alle jordens folk velsignes, fordi du lød mitt ord.
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19 Så gikk Abraham tilbake til sine drenger, og de brøt op og drog sammen til Be'erseba; og Abraham blev boende i Be'erseba.
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
20 Nogen tid derefter kom det nogen og sa til Abraham: Din bror Nakor og Milka har også fått sønner:
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
21 Us, den eldste, og Bus, hans bror, og Kemuel, far til Aram,
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22 og Kesed og Haso og Pildas og Jidlaf og Betuel.
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23 Og Betuel var far til Rebekka. Disse åtte barn fikk Nakor, Abrahams bror, med Milka.
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
24 Også hans medhustru, som hette Re'uma, fikk barn: Tebah og Gaham og Tahas og Ma'aka.
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.

< 1 Mosebok 22 >