< 1 Mosebok 17 >

1 Da Abram var ni og nitti år gammel, åpenbarte Herren sig for ham og sa til ham: Jeg er Gud den allmektige; vandre for mitt åsyn og vær ustraffelig!
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
2 Jeg vil gjøre en pakt mellem mig og dig, og jeg vil gjøre din ætt såre tallrik.
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
3 Da falt Abram på sitt ansikt; og Gud talte med ham og sa:
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
4 Se, jeg gjør en pakt med dig, og du skal bli far til en mengde folk.
“Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
5 Ditt navn skal ikke mere være Abram; men ditt navn skal være Abraham, for jeg gjør dig til far for en mengde folk.
Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
6 Og jeg vil gjøre dig såre fruktbar, så du blir til mange folk, og konger skal utgå fra dig.
Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
7 Og jeg vil oprette en pakt mellem mig og dig og din ætt efter dig, fra slekt til slekt, en evig pakt, så jeg vil være din Gud og Gud for din ætt efter dig.
zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
8 Og jeg vil gi dig og din ætt efter dig det land hvor du bor som fremmed, hele Kana'ans land, til en evig eiendom; og jeg vil være deres Gud.
Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
9 Derefter sa Gud til Abraham: Og du skal holde min pakt, du og din ætt efter dig, fra slekt til slekt.
Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
10 Dette er den pakt mellem mig og eder og din ætt efter dig som I skal holde: Alt mannkjønn hos eder skal omskjæres
Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
11 I skal omskjæres på eders forhud; det skal være tegnet på pakten mellem mig og eder.
Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
12 Åtte dager gammelt skal hvert guttebarn hos eder omskjæres, slekt efter slekt, både den som er født hjemme, og den som er kjøpt for penger, alle som hører til et fremmed folk og ikke er av din ætt.
Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
13 Omskjæres skal både den som er født i ditt hus, og den som er kjøpt for dine penger. Så skal min pakt være på eders kjøtt - en evig pakt.
Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
14 Men en uomskåret av mannkjønn, en hvis forhud ikke blir omskåret, han skal utryddes av sitt folk; han har brutt min pakt.
Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
15 Og Gud sa til Abraham: Sarai, din hustru, skal du ikke lenger kalle Sarai - Sara skal være hennes navn.
Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
16 Og jeg vil velsigne henne, og jeg vil gi dig en sønn også med henne; ja, jeg vil velsigne henne, og hun skal bli til mange folk, konger over folkeslag skal fremgå av henne.
Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
17 Da falt Abraham på sitt ansikt og lo, og han sa ved sig selv: Skulde en som er hundre år gammel, få barn? Og skulde Sara, som er nitti år gammel, føde?
Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
18 Og Abraham sa til Gud: Måtte bare Ismael få leve for ditt åsyn!
Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
19 Da sa Gud: Sannelig, Sara, din hustru, skal føde dig en sønn, og du skal kalle ham Isak, og jeg vil oprette min pakt med ham, en evig pakt for hans ætt efter ham.
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
20 Og Ismael - også om ham har jeg hørt din bønn: Se, jeg vil velsigne ham og gjøre ham fruktbar og gi ham en såre tallrik ætt; tolv høvdinger skal han bli far til, og jeg vil gjøre ham til et stort folk.
Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
21 Men min pakt vil jeg oprette med Isak, som Sara skal føde dig på denne tid næste år.
Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
22 Så holdt han op å tale med ham; og Gud for op igjen fra Abraham.
Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
23 Samme dag tok Abraham Ismael, sin sønn, og alle som var født i hans hus, og alle som var kjøpt for hans penger, alt mannkjønn blandt folkene i Abrahams hus, og omskar deres forhud, således som Gud hadde sagt til ham.
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24 Abraham var ni og nitti år gammel da hans forhud blev omskåret.
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25 Og Ismael, hans sønn, var tretten år da hans forhud blev omskåret.
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26 Denne samme dag blev de omskåret, både Abraham og Ismael, hans sønn;
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27 og alle menn i hans hus, både de som var født hjemme, og de fremmede som var kjøpt for penger. blev omskåret med ham.
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.

< 1 Mosebok 17 >