< Esras 1 >

1 Det var i perserkongen Kyros' første år; da vakte Herren, forat hans ord gjennem Jeremias' munn skulde opfylles, slike tanker i perserkongen Kyros' ånd at han lot utrope i hele sitt rike og dessuten kunngjøre ved en skrivelse:
A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
2 Så sier Kyros, kongen i Persia: Herren, himmelens Gud, har gitt mig alle jordens riker, og han har pålagt mig å bygge ham et hus i Jerusalem i Juda.
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
3 Er det nogen blandt eder av alt hans folk, så være hans Gud med ham, og han kan dra op til Jerusalem i Juda og bygge Herrens, Israels Guds hus! Han er den Gud som bor i Jerusalem.
Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
4 Og alle som ennu er i live, skal folkene på hvert sted hvor de opholder sig som fremmede, understøtte med sølv og gull, med gods og buskap, foruten de frivillige gaver til Guds hus i Jerusalem.
Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
5 Da gjorde Judas og Benjamins familiehoder og prestene og levittene - alle i hvis ånd Gud vakte slike tanker, sig rede til å dra op for å bygge Herrens hus i Jerusalem.
Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
6 Og alle som bodde rundt omkring dem, understøttet dem med sølvkar og gull og gods og buskap og kostbare ting, foruten alt det de gav frivillig.
Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
7 Og kong Kyros lot hente frem de kar som hadde tilhørt Herrens hus, men som Nebukadnesar hadde ført bort fra Jerusalem og satt inn i sin guds hus.
Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
8 Dem lot nu kongen i Persia Kyros hente frem under tilsyn av skattmesteren Mitredat, og han overgav dem efter tall til Sesbassar, Judas fyrste.
Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
9 Tallet på dem var: tretti gullfat, tusen sølvfat, ni og tyve offerkniver,
Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
10 tretti gullbeger, fire hundre og ti sølvbeger av næst beste slag og tusen andre kar.
Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
11 Karene av gull og sølv var i alt fem tusen og fire hundre. Alt dette førte Sesbassar med sig da de bortførte drog op fra Babel til Jerusalem.
Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.

< Esras 1 >