< Esekiel 5 >

1 Og du menneskesønn, ta dig et skarpt sverd! Bruk det som en rakekniv og la det gå over ditt hode og skjegg, og ta dig så en skålvekt og del både hår og skjegg.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 En tredjedel skal du brenne op midt i byen, når kringsetningsdagene er til ende, og en tredjedel skal du ta og hugge i med sverdet rundt omkring byen, og en tredjedel skal du sprede for vinden, og med draget sverd vil jeg forfølge dem.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 Men nogen få hår skal du ta unda, og dem skal du knytte inn i dine kjortelfliker,
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 og av dem skal du igjen ta nogen og kaste dem midt i ilden og brenne dem op; derfra skal det gå ut ild til alt Israels hus.
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 Så sier Herren, Israels Gud: Dette Jerusalem satte jeg midt iblandt hedningefolkene og la land rundt omkring det;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 men det var gjenstridig mot mine lover, så det var mere ugudelig enn hedningefolkene, og mot mine bud, så det var mere ugudelig enn landene rundt omkring det; for de forkastet mine lover og fulgte ikke mine bud.
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 Derfor sier Herren, Israels Gud, så: Fordi I har rast verre enn folkene som bor rundt omkring eder, fordi I ikke har fulgt mine bud og ikke gjort efter mine lover og ikke engang gjort efter de folks lover som bor rundt omkring eder,
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 derfor sier Herren, Israels Gud, så: Se, jeg kommer over dig, jeg og, og jeg vil holde dom hos dig for folkenes øine,
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 og jeg vil gjøre med dig hvad jeg ikke før har gjort og aldri mere vil gjøre maken til - for alle dine vederstyggeligheters skyld.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 Derfor skal foreldre ete sine barn hos dig, og barn ete sine foreldre, og jeg vil holde dom hos dig og sprede alt som blir igjen av dig, for alle vinder.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 Derfor, så sant jeg lever, sier Herren, Israels Gud, sannelig, fordi du har gjort min helligdom uren med alle dine avskyeligheter og alle dine vederstyggeligheter, så vil også jeg vende mitt øie bort fra dig uten skånsel og ikke spare dig.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 Tredjedelen av dig skal dø av pest og fortæres av hunger midt i dig, og tredjedelen skal falle for sverd rundt omkring dig, og tredjedelen vil jeg sprede for alle vinder og forfølge med draget sverd.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 Og min vrede skal uttømmes, og jeg vil stille min harme på dem og ta hevn, og de skal kjenne at jeg, Herren, har talt i min nidkjærhet, når jeg uttømmer min harme på dem.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 Og jeg vil gjøre dig til en ørken og til en spott blandt folkene som bor rundt omkring dig, for øinene på hver den som går forbi.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 Du skal bli til spott og hån, til en advarsel og en forferdelse for folkene som bor rundt omkring dig, når jeg holder dom over dig med vrede og harme og med harmfulle tuktelser - jeg, Herren, har talt -
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 når jeg sender inn blandt dem hungerens onde piler, som er til ødeleggelse, dem som jeg sender for å ødelegge eder, når jeg hoper op hunger over eder og sønderbryter brødets stav for eder.
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 Jeg vil sende hunger over eder og ville dyr, og de skal gjøre dig barnløs, og pest og blod skal gå over dig, og sverd vil jeg la komme over dig; jeg, Herren, har talt.
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Esekiel 5 >