< Esekiel 29 >

1 I det tiende år, i den tiende måned, på den tolvte dag i måneden, kom Herrens ord til mig, og det lød så:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menneskesønn! Vend ditt åsyn mot Farao, Egyptens konge, og spå mot ham og mot hele Egypten!
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Tal og si: Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg kommer over dig, Farao, Egyptens konge, du det store sjøuhyre, som ligger midt i dine strømmer, som sier: Mig tilhører min strøm, jeg har selv gjort den.
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Jeg vil legge kroker i dine kjever og la fiskene i dine strømmer henge fast i dine skjell, og jeg vil dra dig op av dine strømmer, både dig og alle fiskene i dine strømmer, som henger fast i dine skjell.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 Og jeg vil kaste dig ut i ørkenen, både dig og alle fiskene i dine strømmer; på marken skal du falle; du skal ikke samles og ikke sankes; jeg gir dig til føde for jordens dyr og himmelens fugler.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 Og alle Egyptens innbyggere skal kjenne at jeg er Herren, fordi de har vært en rørstav for Israels hus;
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 når de tar dig ved ditt håndfang, så knekkes du og kløver skulderen på dem alle, og når de støtter sig på dig, brytes du i stykker og får lendene på dem alle til å vakle.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Derfor sier Herren, Israels Gud, så: Se, jeg lar sverd komme over dig, og jeg vil utrydde både folk og fe hos dig.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 Og Egyptens land skal bli til en ørken, et øde land, og de skal kjenne at jeg er Herren, fordi han sa: Strømmen hører mig til, jeg har gjort den.
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Se, derfor kommer jeg over dig og dine strømmer, og jeg vil gjøre Egyptens land til en øde ørken, full av grusdynger, fra Migdol til Syene og like til Etiopias grense.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Ingen menneskefot skal fare frem der, og ingen fefot skal fare frem der, og det skal ikke reise sig igjen på firti år.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 Og jeg vil gjøre Egyptens land til en ørken blandt ødelagte land, og dets byer skal ligge øde blandt ødelagte byer i firti år, og jeg vil sprede egypterne blandt folkene og strø dem ut i landene.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 For så sier Herren, Israels Gud: Når firti år er gått, vil jeg samle egypterne fra de folk som de var spredt iblandt.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 Jeg vil gjøre ende på Egyptens fangenskap og føre dem tilbake til landet Patros, det land som de stammer fra, og der skal de være et ringe kongerike.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 Det skal være ringere enn andre kongeriker og ikke mere ophøie sig over folkene, og jeg vil gjøre dem fåtallige, så de ikke skal herske over folkene.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 Og for Israels hus skal det ikke mere være en tilflukt, som minner mig om deres misgjerning, når de vender sig til dem, og de skal kjenne at jeg er Herren, Israels Gud.
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 I det syv og tyvende år, i den første måned, på den første dag i måneden, kom Herrens ord til mig, og det lød så:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Menneskesønn! Nebukadnesar, Babels konge, har latt sin hær utføre et svært arbeid mot Tyrus; hvert hode er skallet og hver skulder slitt. Men lønn har han og hans hær ikke fått av Tyrus for det arbeid han har utført imot det.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Derfor sier Herren, Israels Gud, så: Se, jeg gir Egyptens land til Nebukadnesar, Babels konge, og han skal føre bort dets rikdom og rane og røve alt hvad der er å rane og røve, og det skal hans hær ha til lønn.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Som lønn for det arbeid han har utført, gir jeg ham Egyptens land; for de har arbeidet for mig, sier Herren, Israels Gud.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Den samme dag vil jeg la et horn vokse op for Israels hus, og dig vil jeg gi en oplatt munn midt iblandt dem, og de skal kjenne at jeg er Herren.
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Esekiel 29 >